ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkawarin Da Tinubu Ya Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya bai wa ma’aikata tabba-cin samun kyakykyawan rayuwa a gwamnatinsa.

Ya ce zai ba su fiye da mafi karancin albashi da za su iya gudanar da rayuwarsu da ta iyalansu.

  • Na Gwammace Zama Mashawarci A Gefe, Ba Shugaban Ma’aikatan Tinubu Ba – El-Rufai

Ya kuma yi alkawarin zama amintaccen aminin ma’aikatan kasar nan da zaran an rantsar da gwamnatinsa a ranar 29 ga Mayun 2023.

ADVERTISEMENT

Wadannan alkawuran na kunshe ne a cikin sakon bikin ranar ma’aikata na wan-nan shikerar da ya sanya wa hannu.

Da yake tabbatar wa ma’aikatan kasar nan ta hannun kungiyar kwadago (NLC) da kuma kungiyar ‘yan kasuwa (TUC), Tinubu cewa “Da zarar an rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu a matsayin shugaban Nijeriya, ma’aikata za su samu fiye da mafi karancin albashi. Za ku sami albashi fiye da mafi karancin albashi da za ku iya gudanar da rayuwarku da ta iyalanku.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

“A karkashin shugabancina, za ku sami ‘yanci da walwalan aiki wajen yakir rashin adalci na zamantakewa da tattalin arziki ga daukacin ‘yan Nijeriya, gami da duk ma’aikata.

“Yakinku zai zama yakina, saboda a ko da yaushe ni zan muku yaki. Ina da shirye-shiryen inganta walwala da yanayin aiki mai kyau a cikin ajandar gwamnatina, saboda samar da ingantaccen Nijeriya.

Alkawari ne akai na tun lokacin da aka hai-fe nake kokarin yadda za a inganta rayuwar ma’aikata.”

Da yake kiran hadin kan ma’aikata, Tinubu ya shawarce su da cewa, “Kwanaki masu zuwa, ana bukatar fahimtar juna da hadin kai daga kowane bangare, saboda shugabanci na bukaci mu dauki tsauraren matakai domin jama’armu da ma’aikatan Nijeriya su samu rayuwa mai inganci.”

Zababben shugaban kasar ya nemi goyon daukacin ma’aikatan Nijeriya, inda ya nemi ma’aikata da su hada kai da gwamnatinsa mai jiran gado wajen yakir fatara, jahilci, cututtuka, rashin hadin kai, kabilanci da mambancin addini da duk wani mummunan lamari da ka iya barazana ga zaman lafiya da hadin kan kasa.

Tinubu ya yaba da irin rawar da ma’aikatan Nijeriya suke takawa wajen gina kasa.
Ya ce, “Na bi sahun sauran kasashen duniya da sauran ‘yan’uwa domin murnar ranar ma’aikata ta duniya ta bana. Yau rana ce ta musamman a mafi yawan kasashen duniya, rana ce ta gaisuwa da karrama ma’aikatan da kwazonsu da guminsu ke ci gaba da rura wutar ci gaban Bil’adama.

“Wannan rana tana da matukar mahimmanci ta fuskoki da yawa. Rana ce da aka kirkira saboda gwagwarmayar neman hakkin ma’aikata da ‘yancinsu na zaman-takewa da tattalin arziki. Tun daga shekara ta 1891, aka fara bikin wannan rana a duk fadin duniya.

“A Nijeriya, kowace ranar 1 ga Mayu rana ce ta musamman a kalandar kasarmu. Ranar hutu ce ga al’umma da muke yi ba wai don tunawa da gudunmawa da sa-daukarwar da ma’aikata suke bayarwa ba ne don ci gaban kasarmu ce.

Ta kasance ranar bikin hakkin ma’aikata da kare mutuncisu da ingantaccen albashi da rayuwa mai kyau, kuma mafi mahimmanci shi ne, muhimmiyar rawar da kungiyar kwadago ke takawa wajen hadin kan kasarmu.

“Tun a shekarar 1945 lokacin da ma’aikatan jirgin kasa da wasu kungiyoyin ma’aikatan gwamnati 16 suka jagoranci yajin aikin farko na neman karin albashi sakamakon tsadar rayuwa, kungiyar kwadago a Nijeriya a ko da yaushe tana yaki domin talakawan kasarmu.

Ba abin mamaki ba ne cewa kungiyar ta kara kuzari ga gwagwarmayar neman ‘yancin kai ta hanyar hada kai da masu kishin kasa irin su Nnamdi Azikiwe, Herbert Macaulay, Ahmadu Bello, Obafemi Awolowo, Ernest Ikoli da Anthony Enahoro da sauransu.

“Haka kuma an samu kungiyar kwadago a Nijeriya ne a daidai lokacin da muke gwagwarmayar maido da mulkin dimokuradiyya. Kungiyar kwadago ta Nijeriya da kungiyoyin da ke da alaka da ita kamar irin su NUPENG, Tedtile, PENGASSAN, da dai sauransu, sun hada kai da shugabanni da kungiyoyi masu fafutukar tabba-tar da dimokuradiyya wajen maido da mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a shekarar 1999 bayan kusan shekaru biyu na mulkin kama-karya na sojoji.”

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

'Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.