• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da manoma a fadin wannan kasa ke shirye-shiryen fara noman bana, wasu yankuna a Jihar Neja ba za su samu damar yin noman banan ba.

Wannan lamari, ya faru ne, sakamakon ambaliyar ruwan sama da ta lalata gonakin nasu.

  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Bashir Zuntu A Matsayin Babban Akanta Na Jihar Kaduna
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi

Yankunan da lamarin ya shafa, sun hada da Muye, Apataku, Egba, Ebwa, Bina, Achiba, Dere, Cheku, Sokun da kuma Arah.

Kazalika, akwai kuma matsalar ambaliyar ruwa daga Kogin Gurara, wanda hakan ya tilasta manoman barin gonakinsu da kuma sana’ar kamun Kifi.

Gonakin, wadanda da damansu a baya suka yi fice wajen noman amfani Rogo, Masara, Shinkafa da sauran makamantansu, yanzu manoman sun yi watsi da su.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Wasu daga cikin manoman a wadanan yankuna sun bayyana cewa, sun koma neman wasu gonakin da za su yi shuka ko dai a cikin jihar ko kuma a wasu guraren daban, musamman duba da cewa; sun dogara ne a kan wadannan sana’o’i na noma da kamun Kifi.

Koda-yake dai, gwamnatin tarayya ta yi wani gini mai tsawon zurfin kimanin mita bakwai da nufin dakile ambaliyar ruwan daga Kogi, amma tuni ginin ya rushe tun daga farkon aikin.

An dai gaza sake yin aikin ginin, yau kusan shekara uku zuwa hudu.

Bugu da kari, tuni wasu gonaki, musamman a yankin na Muye da ake da kadada 2.6, aikin yin noma ya tsaya cak, inda kuma mazauna yankin a halin yanzu ke zuwa wasu guraren, domin hada-hadar saye da sayarwar amfanin gona.

Wani mazaunin yankin, Ebwa Ibrahim Saidu ya sanar da cewa; akwai bukatar samar da daukin gaggawa a kan wannan matsala.

“Wasu manoma a yankin, sun koma wasu yankunan, domin neman gonakin da za su yi noma, domin ba za iya sake yin wani noma a gonakin nasu ba, sakamakon faruwar wannan matsala,” in ji Ibrahim.

Ya ce, akasarin matasanmu yanzu, sun koma Jihar Kogi don yin harkar Achaba.

Shi ma Dagacin Muye, Alhaji Salihu Muhammad ya tabbatar da wannan matsala.

“An yi aikin sake gina madatsar ruwar ne, tun bayan shekara uku zuwa hudu da suka gabata, wacce kuma ta sake rushewa a lokacin kakar noman bara, wanda hakan ya jawo lalata gonakinmu da dama“.

“Gwamnatocin baya, sun yi kokrin sake gina madatsar ruwan, amma idan Kogin ya yi ambaliya, sai ta sake lalacewa“ in ji Salihu.

Kazalika, Mukaddashin Manajan Darakta na Riko a Hukumar Samar da Wutar Lantarki ta Kasa (N-HYPPADEC), Mista Jimoh Haruna Gabi, a lokacin kaddamar da sake aikin ginin madatsar ruwan ya sanar da cewa, aikin zai lakume sama da Naira miliyan 600.

Ya kara da cewa, hukumar ta sake gyara kadadar noma 2.6, domin manona su sake komawa gonakinsu, don fara nomansu.

A cewarsa, sake aikin na madatsar ruwan, ana sa ran kammalawa a watan Yuli, kafin ruwan sama ya fara sauka a watan Agusta.

Shi ma, dan Majalisa mai wakiltar mazabar Agaie/Lapai ta tarayya Abdullahi Mahmud, ya bukaci a samar wa da manoman wadannan yankunan dauki, musamman duba da cewa; sana’ar noma ce akasarin al’ummar wadannan yankuna, suka mayar da hankali a kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Yi Alƙawarin Kwato Dazuzzuka Daga Hannun Ƴan Bindiga

Next Post

Jami’ar Tarayya Ta FUGA Ta Kirkiro Da Injin Kyankyasar ‘Yan Tsaki

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

1 day ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Jami’ar Tarayya Ta FUGA Ta Kirkiro Da Injin Kyankyasar ‘Yan Tsaki

Jami’ar Tarayya Ta FUGA Ta Kirkiro Da Injin Kyankyasar ‘Yan Tsaki

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.