ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
Ambaliya

A yayin da manoma a fadin wannan kasa ke shirye-shiryen fara noman bana, wasu yankuna a Jihar Neja ba za su samu damar yin noman banan ba.

Wannan lamari, ya faru ne, sakamakon ambaliyar ruwan sama da ta lalata gonakin nasu.

  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Bashir Zuntu A Matsayin Babban Akanta Na Jihar Kaduna
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi

Yankunan da lamarin ya shafa, sun hada da Muye, Apataku, Egba, Ebwa, Bina, Achiba, Dere, Cheku, Sokun da kuma Arah.

ADVERTISEMENT

Kazalika, akwai kuma matsalar ambaliyar ruwa daga Kogin Gurara, wanda hakan ya tilasta manoman barin gonakinsu da kuma sana’ar kamun Kifi.

Gonakin, wadanda da damansu a baya suka yi fice wajen noman amfani Rogo, Masara, Shinkafa da sauran makamantansu, yanzu manoman sun yi watsi da su.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Wasu daga cikin manoman a wadanan yankuna sun bayyana cewa, sun koma neman wasu gonakin da za su yi shuka ko dai a cikin jihar ko kuma a wasu guraren daban, musamman duba da cewa; sun dogara ne a kan wadannan sana’o’i na noma da kamun Kifi.

Koda-yake dai, gwamnatin tarayya ta yi wani gini mai tsawon zurfin kimanin mita bakwai da nufin dakile ambaliyar ruwan daga Kogi, amma tuni ginin ya rushe tun daga farkon aikin.

An dai gaza sake yin aikin ginin, yau kusan shekara uku zuwa hudu.

Bugu da kari, tuni wasu gonaki, musamman a yankin na Muye da ake da kadada 2.6, aikin yin noma ya tsaya cak, inda kuma mazauna yankin a halin yanzu ke zuwa wasu guraren, domin hada-hadar saye da sayarwar amfanin gona.

Wani mazaunin yankin, Ebwa Ibrahim Saidu ya sanar da cewa; akwai bukatar samar da daukin gaggawa a kan wannan matsala.

“Wasu manoma a yankin, sun koma wasu yankunan, domin neman gonakin da za su yi noma, domin ba za iya sake yin wani noma a gonakin nasu ba, sakamakon faruwar wannan matsala,” in ji Ibrahim.

Ya ce, akasarin matasanmu yanzu, sun koma Jihar Kogi don yin harkar Achaba.

Shi ma Dagacin Muye, Alhaji Salihu Muhammad ya tabbatar da wannan matsala.

“An yi aikin sake gina madatsar ruwar ne, tun bayan shekara uku zuwa hudu da suka gabata, wacce kuma ta sake rushewa a lokacin kakar noman bara, wanda hakan ya jawo lalata gonakinmu da dama“.

“Gwamnatocin baya, sun yi kokrin sake gina madatsar ruwan, amma idan Kogin ya yi ambaliya, sai ta sake lalacewa“ in ji Salihu.

Kazalika, Mukaddashin Manajan Darakta na Riko a Hukumar Samar da Wutar Lantarki ta Kasa (N-HYPPADEC), Mista Jimoh Haruna Gabi, a lokacin kaddamar da sake aikin ginin madatsar ruwan ya sanar da cewa, aikin zai lakume sama da Naira miliyan 600.

Ya kara da cewa, hukumar ta sake gyara kadadar noma 2.6, domin manona su sake komawa gonakinsu, don fara nomansu.

A cewarsa, sake aikin na madatsar ruwan, ana sa ran kammalawa a watan Yuli, kafin ruwan sama ya fara sauka a watan Agusta.

Shi ma, dan Majalisa mai wakiltar mazabar Agaie/Lapai ta tarayya Abdullahi Mahmud, ya bukaci a samar wa da manoman wadannan yankunan dauki, musamman duba da cewa; sana’ar noma ce akasarin al’ummar wadannan yankuna, suka mayar da hankali a kai.

Ambaliya
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Ambaliya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Jami’ar Tarayya Ta FUGA Ta Kirkiro Da Injin Kyankyasar ‘Yan Tsaki

Jami’ar Tarayya Ta FUGA Ta Kirkiro Da Injin Kyankyasar ‘Yan Tsaki

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.