• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 23, Mutane 116,000 Sun Rasa Muhallansu A Benuwe

by Sadiq
3 years ago
Ambaliyar Ruwa

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Benuwe (SEMA), ta ce akalla mutane 23 ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a jihar tun bayan faduwar damina. 

Sakataren zartarwa, Dakta Emmanuel Shior ne, ya sanar da hakan yayin da yake kaddamar da rabon kayan agaji ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a ranar Talata a Makurdi.

  • Da Dumi-Dumi: APC Ta Dage Ranar Fara Yakin Neman Zabenta
  • Adadin Kudin Shigar Kayayyakin Manhajar Masana’antun Sin A Watanni 7 Na Farkon Bana Ya Karu Da Kaso 8.7 Bisa Dari

Ya ce mutane 116,084 ne kuma suka rasa matsugunansu sakamakon ambaliyar ruwa da ta afku a wasu sassan jihar.

“Mutane 74 na fama da raunuka daban-daban. 14 daga cikin 23 da sun mutu a sakamakon hatsarin kwale-kwale a karamar hukumar Guma,” inji shi.

Sakataren zartaswar ya kuma bayyana cewa kawo yanzu ambaliyar ta shafi gonaki hekta 14,040 yayin da gidaje 4,411 suka nutse.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

“Makaranta da kasuwanni, kamfanoni, gidaje da filayen noma da ke yankuna 104 abin ya shafa,” in ji shi.

Ya lissafa kananan hukumomin da abin ya shafa kamar haka, Guma, Vandeikya, Otukpo, Katsina-ala, Makurdi, Apa, Agatu, Tarka, Gboko, Gwer-West da Logo.

“Wadanda abin ya shafa na bukatar agajin gaggawa. Wannan shi ne dalilin wannan aiki namu.

“Mun fara ne da Makurdi da Agatu saboda su ne suke da mutane 34 da 28 da abin ya shafa.

“Wadanda abin ya rutsa da su a Agatu da a halin yanzu suka fake a babbar hanyar tarayya nan ba da jimawa ba za a koma Obagaji,” in ji shi.

Shima da yake jawabi a wajen taron, babban jami’in bincike da ceto na hukumar bada agajin gaggawa ta kasa, John Digah, ya ce hukumar ta tura na’urar kula da ruwa domin tallafa wa wadanda abin ya shafa da ruwan sha.

Digah ya ce na’urar tana da karfin maganin lita 2,000 na ruwa a cikin sa’a guda.

“A cikin kwanaki biyun da suka gabata mun yi jinya tare da raba wa wadanda abin ya shafa ruwan lita 140,000,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Nune-nune Mai Taken “Yin Kokari A Sabon Zamani”

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Nune-nune Mai Taken “Yin Kokari A Sabon Zamani”

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.