• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Lamido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya gargadi Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi taka tsantsan wajen yin amfani da karfin gwamnati don gurgunta jam’iyyun adawa, yana mai cewa irin wadannan ayyukan na iya kawo masa matsala a 2027.

Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wata hira ta musamman da ya yi da manema labarai a garin Birninkudu da ke karamar hukumarsa, jim kadan bayan an zabe shi a matsayin wakilin kasa don wakiltar karamar hukumar Birninkudu a babban taron jam’iyyar PDP mai zuwa.

  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Yunwa Ta Kazanta A Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira Tun Bayan Da Majalisar Dinkin Duniya Ta Dakatar Da Ayyukanta

Alhaji Sule Lamido ya nuna damuwarsa kan yadda ake zargin jam’iyyar APC da Shugaba Tinubu ke amfani da cibiyoyin gwamnati wajen yin barazana, cin zarafi, da kuma raunana jam’iyyun adawa a shirye-shiryen tsayawa takara a wa’adi na biyu a 2027. Ya bayyana wadannan ayyukan a matsayin illa ga shugaban kasa da tsarin siyasa.

A matsayinsa na daya daga cikin iyayen da suka kafa jam’iyyar PDP kuma mamba a kwamitin amintattu, Lamido ya ce, “Idan ka kalli yadda mutane ke ficewa daga PDP, abin takaici ne kuma barazana ce ga kasar nan.

“Kasar da dimokuradiyya ke cikin babban hadari saboda tarwatsa ‘yan adawa ta amfani da cibiyoyin gwamnati kamar INEC, ‘yansanda, DSS, da EFCC, ba wai kawai kuna tarwatsa ‘yan adawarku ba har ma da kanku.”

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ya kara da cewa, “An gina tushen dimokuradiyya a kan ‘yanci, da adawa. Tinubu, a cikin hikimarsa, ya yi imanin cewa ta hanyar lalata jam’iyyun adawa kamar PDP, yana bunkasa arzikinsa na siyasa. “Abin takaici, yana da wayo dan kadan, saboda tarwatsa PDP a matsayin jam’iyyar siyasa yana nufin za a lalata Nijeriya da kanta, kuma komai zai ruguje a kansa.”

Lamido ya bayyana kwarin gwiwar cewa wadanda suka bar PDP za su dawo. “Kawai jira watanni biyar ko shida, kuma a karshen wannan shekarar, za ku gani. Tinubu ya kashe kansa a siyasa. Wadanda ke tare da shi ma suna kashe kansu a siyasa.

Ya kara da cewa, “Jam’iyyar siyasa ko ta yaya ya kamata ta iya kare kanta daga ‘yan adawa. Idan APC tana aiki, wannan ba matsala ba ce. Amma lokacin da gwamnati da shugaban kasa ke yaki da PDP, wannan yana da hadari. PDP a matsayinta na jam’iyyar adawa za ta iya yaki da jam’iyyar APC mai mulki, kuma APC za ta iya yaki da mu. Amma idan duk gwamnatin tarayya ta yi amfani da kayan aikinta don yaki da mu, wannan shi ne ainihin hadari. ”

Lamido ya ci gaba da cewa, “Ba APC ce ke yaki da mu ba, gwamnati ce ke yaki da mu. Tinubu ne a matsayinsa na shugaban kasa yake yaki da mu. Idan ya lalata tsarin, kawai yana gayyatar kashe kansa a siyasa. Wadanda ke biye da shi suna tsoron EFCC. Amma me ya sa ake jin tsoron EFCC? Idan kun tuna abin da Ribadu ya fada game da Shugaba Tinubu shekaru da suka wuce, me ya sa zan ji tsoronsa? “Saboda EFCC ta fallasa shi a baya, ta yaya zan ji tsoronsa?”

Ya nuna godiya da farin cikinsa game da aikin da jam’iyyar da mambobinta suka yi saboda girmama shi da ba shi mukami.

Alhaji Lamido ya kuma yaba wa PDP da kwamitin zaben bisa kyakkyawan aikin da suka yi, tare da gode wa mambobin da suka gudanar cikin tsari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Gabon

Next Post

Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

5 days ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

5 days ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

2 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

3 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

4 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

4 weeks ago
Next Post
Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.