• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Lamido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya gargadi Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi taka tsantsan wajen yin amfani da karfin gwamnati don gurgunta jam’iyyun adawa, yana mai cewa irin wadannan ayyukan na iya kawo masa matsala a 2027.

Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wata hira ta musamman da ya yi da manema labarai a garin Birninkudu da ke karamar hukumarsa, jim kadan bayan an zabe shi a matsayin wakilin kasa don wakiltar karamar hukumar Birninkudu a babban taron jam’iyyar PDP mai zuwa.

  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Yunwa Ta Kazanta A Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira Tun Bayan Da Majalisar Dinkin Duniya Ta Dakatar Da Ayyukanta

Alhaji Sule Lamido ya nuna damuwarsa kan yadda ake zargin jam’iyyar APC da Shugaba Tinubu ke amfani da cibiyoyin gwamnati wajen yin barazana, cin zarafi, da kuma raunana jam’iyyun adawa a shirye-shiryen tsayawa takara a wa’adi na biyu a 2027. Ya bayyana wadannan ayyukan a matsayin illa ga shugaban kasa da tsarin siyasa.

A matsayinsa na daya daga cikin iyayen da suka kafa jam’iyyar PDP kuma mamba a kwamitin amintattu, Lamido ya ce, “Idan ka kalli yadda mutane ke ficewa daga PDP, abin takaici ne kuma barazana ce ga kasar nan.

“Kasar da dimokuradiyya ke cikin babban hadari saboda tarwatsa ‘yan adawa ta amfani da cibiyoyin gwamnati kamar INEC, ‘yansanda, DSS, da EFCC, ba wai kawai kuna tarwatsa ‘yan adawarku ba har ma da kanku.”

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Ya kara da cewa, “An gina tushen dimokuradiyya a kan ‘yanci, da adawa. Tinubu, a cikin hikimarsa, ya yi imanin cewa ta hanyar lalata jam’iyyun adawa kamar PDP, yana bunkasa arzikinsa na siyasa. “Abin takaici, yana da wayo dan kadan, saboda tarwatsa PDP a matsayin jam’iyyar siyasa yana nufin za a lalata Nijeriya da kanta, kuma komai zai ruguje a kansa.”

Lamido ya bayyana kwarin gwiwar cewa wadanda suka bar PDP za su dawo. “Kawai jira watanni biyar ko shida, kuma a karshen wannan shekarar, za ku gani. Tinubu ya kashe kansa a siyasa. Wadanda ke tare da shi ma suna kashe kansu a siyasa.

Ya kara da cewa, “Jam’iyyar siyasa ko ta yaya ya kamata ta iya kare kanta daga ‘yan adawa. Idan APC tana aiki, wannan ba matsala ba ce. Amma lokacin da gwamnati da shugaban kasa ke yaki da PDP, wannan yana da hadari. PDP a matsayinta na jam’iyyar adawa za ta iya yaki da jam’iyyar APC mai mulki, kuma APC za ta iya yaki da mu. Amma idan duk gwamnatin tarayya ta yi amfani da kayan aikinta don yaki da mu, wannan shi ne ainihin hadari. ”

Lamido ya ci gaba da cewa, “Ba APC ce ke yaki da mu ba, gwamnati ce ke yaki da mu. Tinubu ne a matsayinsa na shugaban kasa yake yaki da mu. Idan ya lalata tsarin, kawai yana gayyatar kashe kansa a siyasa. Wadanda ke biye da shi suna tsoron EFCC. Amma me ya sa ake jin tsoron EFCC? Idan kun tuna abin da Ribadu ya fada game da Shugaba Tinubu shekaru da suka wuce, me ya sa zan ji tsoronsa? “Saboda EFCC ta fallasa shi a baya, ta yaya zan ji tsoronsa?”

Ya nuna godiya da farin cikinsa game da aikin da jam’iyyar da mambobinta suka yi saboda girmama shi da ba shi mukami.

Alhaji Lamido ya kuma yaba wa PDP da kwamitin zaben bisa kyakkyawan aikin da suka yi, tare da gode wa mambobin da suka gudanar cikin tsari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Gabon

Next Post

Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.