• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Salon Diflomasiyyar Kasar Sin Zai Iya Sulhunta ECOWAS Da Kasashen Nijar, Mali Da Burkina Faso Cikin Sauki

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Amfani Da Salon Diflomasiyyar Kasar Sin Zai Iya Sulhunta ECOWAS Da Kasashen Nijar, Mali Da Burkina Faso Cikin Sauki

{"ARInfo":{"IsUseAR":false},"Version":"1.0.0","MakeupInfo":{"IsUseMakeup":false},"FaceliftInfo":{"IsChangeEyeLift":false,"IsChangeFacelift":false,"IsChangePostureLift":false,"IsChangeNose":false,"IsChangeFaceChin":false,"IsChangeMouth":false,"IsChangeThinFace":false},"BeautyInfo":{"SwitchMedicatedAcne":false,"IsAIBeauty":false,"IsBrightEyes":false,"IsSharpen":false,"IsOldBeauty":false,"IsReduceBlackEyes":false},"HandlerInfo":{"AppName":2},"FilterInfo":{"IsUseFilter":false}}

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kullum na tuna da wakar “Hada Kanmu Afirka Mu So Juna” na marigayi Malam Abubakar Ladan Zariya sai na ji takaicin irin bahallatsar da aka samu a tsakanin kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso da Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma (ECOWAS), sakamakon kifar da gwamnatocin fararen hula a wadannan kasashen.

 

Bayan kurar barazanar daukar matakin sojin ECOWAS a kan Nijar ta lafa, a watan Janairun bana, Mali da Burkina Faso da kuma Nijar suka fito karara suka yi fatali da tayin sake dawowa ECOWAS tare da kafa wani hadin kasashensu da suka zartar tare da rattaba hannu a ranar 6 ga Yulin 2024.

  • Google, Microsoft, TikTok Sun Biya Gwamnatin Nijeriya Harajin N2.55trn A 2024 – NITDA
  • Gobara Ta Kone Shaguna A Kasuwar Yobe

Wannan ya sake karya lagon fatan da ake da shi na sake dunkulewar ECOWAS tare da hada karfi da karfe a tsakanin mambobin kasashen wajen fuskantar matsalolinsu na ci gaban tattalin arziki da kyautata zamantakewa. Saboda kasashen uku suna zargin ECOWAS da zama ’yar amshin shatar kasashen yammacin duniya da suka raba-gari da su musamman uwargijiyarsu Faransa.

 

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Masana da masharhanta a yankin Afirka na ci gaba da yekuwar a lalubo bakin zaren sulhu a tsakanin ECOWAS da kasashen. Wannan ya sa hankalina ya karkata ga wani binciken jin ra’ayoyin jama’a da wata kafar yada labarai ta kasar Sin CGTN ta gudanar game da irin tasirin da salon diflomasiyyar kasar Sin ya yi wajen sulhunta kasashen da suka yi baram-baram da juna.

 

Kowa ya san an kwashi tsawon lokaci ana gaba tsakanin kasashen Saudiyya da Iran, duk kuwa da irin kusancin da suke da shi da juna na zama kasashe masu alkibla daya ta musulunci da kasancewarsu ’yan yankin Asiya. Amma bisa amfani da salon diflomasiyya ta kasar Sin, kasashen biyu sun sake amincewa da juna har ma suka yanke shawarar mayar da huldar diflomasiyya a tsakaninsu a ranar 6 ga watan Afrilun 2023 bayan wata ganawa a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

 

Haka nan, shekara daya bayan sulhun Iran da Saudiyya, bisa amfani da salon diflomasiyyarta, kasar Sin ta yi nasarar sake sulhunta bangarorin Falasdinawa na Fatah da Hamas da suke zaman ’yan marina a tsakaninsu ta yadda za su zama tsintsiya madaurinki daya su kuma fuskanci kalubalen yankin Falasdinu bai-daya.

 

Hakika sulhunta gabar da ta shafi akida ba karamar nasara ba ce saboda kowa ya san yadda ake zafafa ta a tsakanin bangarorin da ake yi. Bisa wadannan manyan nasarori da salon diflomasiyyar kasar Sin ya samu baro-baro a fili, ko shakka babu idan aka yi amfani da hakan za a iya daidata hannun-rigar da kasashen Mali, Nijar da Burkina Faso suka yi da ECOWAS. Musamman ganin cewa kowane bangare a cikinsu ya amince da kasar Sin a matsayin mai taimako da kawo alheri ga Afirka.

 

Kuma ba ni kadai nake ganin haka ba. A binciken jin ra’ayoyin da CGTN ta yi game da tasirin salon diflomasiyyar kasar Sin, mutane daga sassan duniya daban-daban sun ba da tabbacin irin tasirin da salon diflomasiyyar kasar Sin ya yi wajen kawo kwanciyar hankali a duniya.

 

Bari mu kawo misalai daga shirye-shiryen da kasar take kawo shawarar aiwatarwa ta hanyar diflomasiyya a tsakanin kasashen duniya domin samun ci gaba na bai-daya. Daga cikin alkaluman da aka tattaro, kaso 82.5 cikin dari na wadanda aka ji ra’ayoyinsu sun ce tsarin da kasar Sin ta zo da shi mai taken “al’umma mai makomar bai-daya domin bil’adama” ya kara zaburar da kokarin gina kyakkyawar makoma ga dan Adam.

 

Haka nan kaso 84.5 cikin dari na masu bayyana ra’ayin sun aminta da shawarar Shawarar Bunkasa Ci Gaban Duniya, inda suka yi amannar cewa samar da ci gaba ita ce hanyar warware matsalolin duniya da samun farin ciki ga dan Adam. Duk wadannan shawarwari daga cikin hikimomin salon diflomasiyya ne na kasar Sin.

 

Don haka, amfani da salon diflomasiyyar kasar zai ba da damar warware takaddamar da ake yi tsakanin ECOWAS da kuma kasashen da suka yi bara’a da ita su uku. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Jihar Adamawa Ta Amince Da Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Gundumomi

Next Post

Tinubu Ya Amince Da Biyan Kuɗin Kafa Cibiyar Yaɗa Labarai Ta UNESCO

Related

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

3 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

4 hours ago
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU
Daga Birnin Sin

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

6 hours ago
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

7 hours ago
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

8 hours ago
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

8 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Amince Da Biyan Kuɗin Kafa Cibiyar Yaɗa Labarai Ta UNESCO

Tinubu Ya Amince Da Biyan Kuɗin Kafa Cibiyar Yaɗa Labarai Ta UNESCO

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.