ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Salon Diflomasiyyar Kasar Sin Zai Iya Sulhunta ECOWAS Da Kasashen Nijar, Mali Da Burkina Faso Cikin Sauki

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
{"ARInfo":{"IsUseAR":false},"Version":"1.0.0","MakeupInfo":{"IsUseMakeup":false},"FaceliftInfo":{"IsChangeEyeLift":false,"IsChangeFacelift":false,"IsChangePostureLift":false,"IsChangeNose":false,"IsChangeFaceChin":false,"IsChangeMouth":false,"IsChangeThinFace":false},"BeautyInfo":{"SwitchMedicatedAcne":false,"IsAIBeauty":false,"IsBrightEyes":false,"IsSharpen":false,"IsOldBeauty":false,"IsReduceBlackEyes":false},"HandlerInfo":{"AppName":2},"FilterInfo":{"IsUseFilter":false}}

{"ARInfo":{"IsUseAR":false},"Version":"1.0.0","MakeupInfo":{"IsUseMakeup":false},"FaceliftInfo":{"IsChangeEyeLift":false,"IsChangeFacelift":false,"IsChangePostureLift":false,"IsChangeNose":false,"IsChangeFaceChin":false,"IsChangeMouth":false,"IsChangeThinFace":false},"BeautyInfo":{"SwitchMedicatedAcne":false,"IsAIBeauty":false,"IsBrightEyes":false,"IsSharpen":false,"IsOldBeauty":false,"IsReduceBlackEyes":false},"HandlerInfo":{"AppName":2},"FilterInfo":{"IsUseFilter":false}}

A kullum na tuna da wakar “Hada Kanmu Afirka Mu So Juna” na marigayi Malam Abubakar Ladan Zariya sai na ji takaicin irin bahallatsar da aka samu a tsakanin kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso da Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma (ECOWAS), sakamakon kifar da gwamnatocin fararen hula a wadannan kasashen.

 

Bayan kurar barazanar daukar matakin sojin ECOWAS a kan Nijar ta lafa, a watan Janairun bana, Mali da Burkina Faso da kuma Nijar suka fito karara suka yi fatali da tayin sake dawowa ECOWAS tare da kafa wani hadin kasashensu da suka zartar tare da rattaba hannu a ranar 6 ga Yulin 2024.

ADVERTISEMENT
  • Google, Microsoft, TikTok Sun Biya Gwamnatin Nijeriya Harajin N2.55trn A 2024 – NITDA
  • Gobara Ta Kone Shaguna A Kasuwar Yobe

Wannan ya sake karya lagon fatan da ake da shi na sake dunkulewar ECOWAS tare da hada karfi da karfe a tsakanin mambobin kasashen wajen fuskantar matsalolinsu na ci gaban tattalin arziki da kyautata zamantakewa. Saboda kasashen uku suna zargin ECOWAS da zama ’yar amshin shatar kasashen yammacin duniya da suka raba-gari da su musamman uwargijiyarsu Faransa.

 

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Masana da masharhanta a yankin Afirka na ci gaba da yekuwar a lalubo bakin zaren sulhu a tsakanin ECOWAS da kasashen. Wannan ya sa hankalina ya karkata ga wani binciken jin ra’ayoyin jama’a da wata kafar yada labarai ta kasar Sin CGTN ta gudanar game da irin tasirin da salon diflomasiyyar kasar Sin ya yi wajen sulhunta kasashen da suka yi baram-baram da juna.

 

Kowa ya san an kwashi tsawon lokaci ana gaba tsakanin kasashen Saudiyya da Iran, duk kuwa da irin kusancin da suke da shi da juna na zama kasashe masu alkibla daya ta musulunci da kasancewarsu ’yan yankin Asiya. Amma bisa amfani da salon diflomasiyya ta kasar Sin, kasashen biyu sun sake amincewa da juna har ma suka yanke shawarar mayar da huldar diflomasiyya a tsakaninsu a ranar 6 ga watan Afrilun 2023 bayan wata ganawa a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

 

Haka nan, shekara daya bayan sulhun Iran da Saudiyya, bisa amfani da salon diflomasiyyarta, kasar Sin ta yi nasarar sake sulhunta bangarorin Falasdinawa na Fatah da Hamas da suke zaman ’yan marina a tsakaninsu ta yadda za su zama tsintsiya madaurinki daya su kuma fuskanci kalubalen yankin Falasdinu bai-daya.

 

Hakika sulhunta gabar da ta shafi akida ba karamar nasara ba ce saboda kowa ya san yadda ake zafafa ta a tsakanin bangarorin da ake yi. Bisa wadannan manyan nasarori da salon diflomasiyyar kasar Sin ya samu baro-baro a fili, ko shakka babu idan aka yi amfani da hakan za a iya daidata hannun-rigar da kasashen Mali, Nijar da Burkina Faso suka yi da ECOWAS. Musamman ganin cewa kowane bangare a cikinsu ya amince da kasar Sin a matsayin mai taimako da kawo alheri ga Afirka.

 

Kuma ba ni kadai nake ganin haka ba. A binciken jin ra’ayoyin da CGTN ta yi game da tasirin salon diflomasiyyar kasar Sin, mutane daga sassan duniya daban-daban sun ba da tabbacin irin tasirin da salon diflomasiyyar kasar Sin ya yi wajen kawo kwanciyar hankali a duniya.

 

Bari mu kawo misalai daga shirye-shiryen da kasar take kawo shawarar aiwatarwa ta hanyar diflomasiyya a tsakanin kasashen duniya domin samun ci gaba na bai-daya. Daga cikin alkaluman da aka tattaro, kaso 82.5 cikin dari na wadanda aka ji ra’ayoyinsu sun ce tsarin da kasar Sin ta zo da shi mai taken “al’umma mai makomar bai-daya domin bil’adama” ya kara zaburar da kokarin gina kyakkyawar makoma ga dan Adam.

 

Haka nan kaso 84.5 cikin dari na masu bayyana ra’ayin sun aminta da shawarar Shawarar Bunkasa Ci Gaban Duniya, inda suka yi amannar cewa samar da ci gaba ita ce hanyar warware matsalolin duniya da samun farin ciki ga dan Adam. Duk wadannan shawarwari daga cikin hikimomin salon diflomasiyya ne na kasar Sin.

 

Don haka, amfani da salon diflomasiyyar kasar zai ba da damar warware takaddamar da ake yi tsakanin ECOWAS da kuma kasashen da suka yi bara’a da ita su uku. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Ecowas
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Ecowas
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Tinubu Ya Amince Da Biyan Kuɗin Kafa Cibiyar Yaɗa Labarai Ta UNESCO

Tinubu Ya Amince Da Biyan Kuɗin Kafa Cibiyar Yaɗa Labarai Ta UNESCO

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.