• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka: Mai Shafawa Sauran Kasashe Bakin Fenti

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Amurka: Mai Shafawa Sauran Kasashe Bakin Fenti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony J. Blinken, a gun “taron kolin Demokuradiyya” da aka gudanar a kwanan baya, ya zargi kasar Sin da gurbata yanayin sadarwa, da yada labarai na jabu. Amma ko hakan gaskiya ne? Alal hakika, wane ne ke yada labaran jabu?

Kowa ya san cewa Amurka kasa ce da ta fi yada labarai na jabu da kirkirarsu. Tun lokacin cacar baka, Amurka ta rika sayen kafofin yada labarai karkashin wani shiri mai suna “Operation Mockingbird” don su yi abin da take so.

  • Kungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’i SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aikin Gargadi Da Suka Shiga
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Kara Amfani Da Filaye Don Bunkasuwar Yankuna Mai Inganci

A shekarun baya-baya nan, ganin yadda Sin ta bunkasa cikin sauri, Amurka ta mai da ita abokiyar takara mafi girma, har ma ta tada yakin bayanai a kanta. Kwanan baya, wani masanin Turai mai suna Jan Oberg ya fayyace cewa, a shekarun baya, majalisar dokokin kasar Amurka ta zartas da wani kudiri na ware kudi har dallar Amurka biliyan 1.5, don horas da‘yan jaridar kasashen yamma cikin tsawon shekaru 5, don su rubuta labaran shafawa kasar Sin bakin fenti. Kaza lika, ba sau daya ba, ‘yan siyasar Amurka ciki har da shugaban hukumar leken asiri ta CIA sun amince cewa, Amurka ta dauki wasu matakai a boye, ciki har da sayen wasu kafofin yada labarai don shafawa kasar Sin bakin fenti, abin da ya shaida cewa, Amurka ta tsai da shirin shafawa Sin bakin fenti cikin dogon lokaci.

Yanzu Sin na samun bunkasuwar tattalin arziki mai karko, amma Amurka ta yada labarai wai tattalin arzikin kasar Sin zai dakushe. A yayin da shawarar “ziri daya da hanya daya” ke amfanar al’ummar kasashe daban-daban, Amurka ta ce wai tarkon bashi ne. A yayin da al’ummar kasashe da dama ke bayyana hakikanin abin da suka ji ko gani a Sin, Amurka ta ce wai Sin ta sayi kafafen yada labarai. Ban da wannan kuma, Amurka ta bayyana matakan da Sin take dauka na bunkasa tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar al’umma a jihar Xinjiang a matsayin aikin tilas da kisan kare dangi. Shin ko Amurka ta fadi gaskiya? Gwano ba ya jin warin jikinsa.

Hausawa kan ce “Munafuncin dodo ya kan ci mai shi”. Amurka tana yunkurin gurbata gaskiya, amma duk da haka sauran kasashe na fahimtar burinta sosai, kuma ba za a amince da hakan ba ko kadan. (Mai zane da rubutu: MINA)

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Waɗanda Suka Mutu Yayin Turmutsutsun Karɓar Sadaƙa Ya Ƙaru Zuwa 7 A Jihar Bauchi

Next Post

Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2 Ya Shiga Falakinsa A Zagayen Wata

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

24 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

3 days ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

1 week ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 weeks ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 weeks ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Next Post
Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2 Ya Shiga Falakinsa A Zagayen Wata

Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2 Ya Shiga Falakinsa A Zagayen Wata

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Amurka

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Amurka

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.