ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka: Mai Shafawa Sauran Kasashe Bakin Fenti

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony J. Blinken, a gun “taron kolin Demokuradiyya” da aka gudanar a kwanan baya, ya zargi kasar Sin da gurbata yanayin sadarwa, da yada labarai na jabu. Amma ko hakan gaskiya ne? Alal hakika, wane ne ke yada labaran jabu?

Kowa ya san cewa Amurka kasa ce da ta fi yada labarai na jabu da kirkirarsu. Tun lokacin cacar baka, Amurka ta rika sayen kafofin yada labarai karkashin wani shiri mai suna “Operation Mockingbird” don su yi abin da take so.

  • Kungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’i SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aikin Gargadi Da Suka Shiga
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Kara Amfani Da Filaye Don Bunkasuwar Yankuna Mai Inganci

A shekarun baya-baya nan, ganin yadda Sin ta bunkasa cikin sauri, Amurka ta mai da ita abokiyar takara mafi girma, har ma ta tada yakin bayanai a kanta. Kwanan baya, wani masanin Turai mai suna Jan Oberg ya fayyace cewa, a shekarun baya, majalisar dokokin kasar Amurka ta zartas da wani kudiri na ware kudi har dallar Amurka biliyan 1.5, don horas da‘yan jaridar kasashen yamma cikin tsawon shekaru 5, don su rubuta labaran shafawa kasar Sin bakin fenti. Kaza lika, ba sau daya ba, ‘yan siyasar Amurka ciki har da shugaban hukumar leken asiri ta CIA sun amince cewa, Amurka ta dauki wasu matakai a boye, ciki har da sayen wasu kafofin yada labarai don shafawa kasar Sin bakin fenti, abin da ya shaida cewa, Amurka ta tsai da shirin shafawa Sin bakin fenti cikin dogon lokaci.

ADVERTISEMENT

Yanzu Sin na samun bunkasuwar tattalin arziki mai karko, amma Amurka ta yada labarai wai tattalin arzikin kasar Sin zai dakushe. A yayin da shawarar “ziri daya da hanya daya” ke amfanar al’ummar kasashe daban-daban, Amurka ta ce wai tarkon bashi ne. A yayin da al’ummar kasashe da dama ke bayyana hakikanin abin da suka ji ko gani a Sin, Amurka ta ce wai Sin ta sayi kafafen yada labarai. Ban da wannan kuma, Amurka ta bayyana matakan da Sin take dauka na bunkasa tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar al’umma a jihar Xinjiang a matsayin aikin tilas da kisan kare dangi. Shin ko Amurka ta fadi gaskiya? Gwano ba ya jin warin jikinsa.

Hausawa kan ce “Munafuncin dodo ya kan ci mai shi”. Amurka tana yunkurin gurbata gaskiya, amma duk da haka sauran kasashe na fahimtar burinta sosai, kuma ba za a amince da hakan ba ko kadan. (Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi
Ra'ayi Riga

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Next Post
Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2 Ya Shiga Falakinsa A Zagayen Wata

Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2 Ya Shiga Falakinsa A Zagayen Wata

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Amurka

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Amurka

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Amurka

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.