ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka: Mai Shafawa Sauran Kasashe Bakin Fenti

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony J. Blinken, a gun “taron kolin Demokuradiyya” da aka gudanar a kwanan baya, ya zargi kasar Sin da gurbata yanayin sadarwa, da yada labarai na jabu. Amma ko hakan gaskiya ne? Alal hakika, wane ne ke yada labaran jabu?

Kowa ya san cewa Amurka kasa ce da ta fi yada labarai na jabu da kirkirarsu. Tun lokacin cacar baka, Amurka ta rika sayen kafofin yada labarai karkashin wani shiri mai suna “Operation Mockingbird” don su yi abin da take so.

  • Kungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’i SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aikin Gargadi Da Suka Shiga
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Kara Amfani Da Filaye Don Bunkasuwar Yankuna Mai Inganci

A shekarun baya-baya nan, ganin yadda Sin ta bunkasa cikin sauri, Amurka ta mai da ita abokiyar takara mafi girma, har ma ta tada yakin bayanai a kanta. Kwanan baya, wani masanin Turai mai suna Jan Oberg ya fayyace cewa, a shekarun baya, majalisar dokokin kasar Amurka ta zartas da wani kudiri na ware kudi har dallar Amurka biliyan 1.5, don horas da‘yan jaridar kasashen yamma cikin tsawon shekaru 5, don su rubuta labaran shafawa kasar Sin bakin fenti. Kaza lika, ba sau daya ba, ‘yan siyasar Amurka ciki har da shugaban hukumar leken asiri ta CIA sun amince cewa, Amurka ta dauki wasu matakai a boye, ciki har da sayen wasu kafofin yada labarai don shafawa kasar Sin bakin fenti, abin da ya shaida cewa, Amurka ta tsai da shirin shafawa Sin bakin fenti cikin dogon lokaci.

ADVERTISEMENT

Yanzu Sin na samun bunkasuwar tattalin arziki mai karko, amma Amurka ta yada labarai wai tattalin arzikin kasar Sin zai dakushe. A yayin da shawarar “ziri daya da hanya daya” ke amfanar al’ummar kasashe daban-daban, Amurka ta ce wai tarkon bashi ne. A yayin da al’ummar kasashe da dama ke bayyana hakikanin abin da suka ji ko gani a Sin, Amurka ta ce wai Sin ta sayi kafafen yada labarai. Ban da wannan kuma, Amurka ta bayyana matakan da Sin take dauka na bunkasa tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar al’umma a jihar Xinjiang a matsayin aikin tilas da kisan kare dangi. Shin ko Amurka ta fadi gaskiya? Gwano ba ya jin warin jikinsa.

Hausawa kan ce “Munafuncin dodo ya kan ci mai shi”. Amurka tana yunkurin gurbata gaskiya, amma duk da haka sauran kasashe na fahimtar burinta sosai, kuma ba za a amince da hakan ba ko kadan. (Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2 Ya Shiga Falakinsa A Zagayen Wata

Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2 Ya Shiga Falakinsa A Zagayen Wata

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.