• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Lahanta Taiwan Na Kasar Sin Ta Hanyar Sayarwa Yankin Da Makamai

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Taiwan

Kwanan baya, shugaban Amurka Joe Biden ya sa hannu kan dokar ba da izinin tsaron kasa ta (NDAA) ta shekarar kasafin kudi ta 2025. Inda ake yanke shawarar ware kudin ayyukan soja da yawansu ya kai dalar biliyan 895, adadin ya kai matsayin koli a tarihin kasar, matakin da ya bayyana burin Washington a bangaren bukatun karuwar kasafin kudin soja.

Dokar tana yunkurin samun daidaito ta hanyar shafawa kasar Sin bakin fenti har fiye da sau 10, inda ta yi ikirarin cewa wai kasar Sin barazana ce, baya ga haka, ta tsoma baki cikin batun yankin Taiwan, ta kuma ingiza manufar samarwa yankin taimakon makamai, wanda hakan tamkar sako ne maras dacewa ga ’yan awaren yankin Taiwan.

  • Mutum 2 Sun Mutu Yayin Da ‘Yansanda Suka Ceto Mutum 10 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 2, Sun Jikkata 3 A Borno

Alal hakika, sau da dama Sin ta sha bayyana matsayin da ta dade tana tsayawa a kai game da batun Taiwan, wato “Muradu masu tushe na kasar Sin, kuma abu mafi muhimmanci ga huldar kasashen biyu”.

A watan da ya gabata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na Amurka Joe Biden, yayin da suke ziyarar aiki a Peru, inda suka tattauna tare da cimma matsaya daya kan dabaru 7, da wasu abubuwa masu muhimmanci 4 da dole ne bangarorin biyu su nacewa.

Daga cikin muhimman abubuwan 4, batun Taiwan ne mafi muhimmanci. Kuma yayin ganawar tasu, Biden ya nanata kin amincewa da sabon salon yakin cacar baka, da kin nuna goyon bayan ’yan awaren yankin Taiwan, da dai sauran alkawura na siyasa. Amma, ba da dadewa ba, Amurka ta yi watsi da alkawarinta, ta nuna fuska biyu kan batun yankin Taiwan, matakin zai haifar da rashin tabbaci ga yankin.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sabuwar gwamnatin Amurka mai jiran gado, za ta fara jan ragamar kasar nan da kwanaki 20 masu zuwa. Dole ne Amurka ta yi taka tsantsan kan batun Taiwan, idan tana son wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, da nacewa ga hadaddun sanarwoyi 3 na tsakanin kasashen biyu, da cika alkawarinta da ta yi game da kasar Sin, da bayyana matsayinta a fili, don gane da adawa da ware Taiwan daga babban yankin Sin, da goyon bayan dunkulewar kasar Sin cikin lumana. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
Ta’addanci

Sojoji Sun Kama Mutane 20 Kan Zargin Kashe-kashe A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.