Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

An Bukaci A Kara Kaimi Wajen Addu’a Kan Matsalar Tsaro

by Muhammad
February 21, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
Matsalar Tsaro
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Muhammad,

Shugaban kungiyar Kiristoci ta kasa reshen jihar Kano Rabaran Adeyemo Adeolu ya bayyana cewa halin rashin tsaro da ake fama da shi abin bakin ciki ne da damuwa a kasarnan.

samndaads

Kuma abin da za a yi dan maganin matsalar shi ne haduwar kan al’ummar dan kauda ‘yan’ta’adda tare da tsayawa da dagewa, akan yin addu’a wanda idan ana yi Ubangiji zai ji kukansu ya bada nasarar kauda matsalolin da ake fama dasu.

Rabaran Adeyemo ya ce, wannan matsalar ta rashin tsaro a gaskiya, kamar wata  gobara ce da za ta iya cin ko’ina idan kuma ba’a mai da hankali ba wurare da babu wannan irin matsala za a iya wayar gari ya shafe su.

Rabaran Adeyemo ya ce, kar al’ummar jihar Kano su gaji da addu’a a hada hannu kuma da irin kokarin da Gwamnan Kano. Dokta Abdullahi Umar Ganduje yake wajen tabbatar da zaman lafiya.

Ya ce, a cigaba da addu’a wannan damuwa kar ya shigo jihar Kano a kuma rika yi wa Gwamnatin  Kano addu’a na  cigaba da samun zaman lafiya a Kano a  cikin fahimtar juna da kauna, kar a yarda wani abu na rashin jin.dadi ya shiga tsakani.Ita kuma Gwamnati yakamata  ta kara nunka kokarinta wajen tsare rayuka da dukiyoyin jama’a, su kuma jama’a su guji yin kalamai da za su kawo gaba a cikin zamantakewa ayi duk abinda zai kara hada kai da kaunar juna a tsakani.

Rabaran Adeyemo Oluade Samuel ya ja hankalin masu wa’azi a Masallatai da coci akan cigaba da yin kira na zaman lafiya, dukkan wa’azinsu ya zama nasa  kaunar juna da zaman lafiya ne idan ana yin haka Allah zai kaunacesu ya mara musu baya karsu zama shugabannin addini da za su rika bakar magana da zai kawo wariya su zama masu hada kan al’umma da koyar da su akan muhimmancin zaman lafiya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Martani: Hukumomin Gwamnatin Tarayya Sun Kashe Naira Biliyan 3.77 Wajen Tafiyarsu Da Iyalansu Saudiyya

Next Post

Kwankwaso Ya Yi Farin Ciki Da Dawowar Dalibai 370 Da Ya Tura Karatu Kasashen Waje

RelatedPosts

Shata Ya Shaida Ma Ni Zan Dade A Bisa Kan Karagar Mulki – Sarkin Ningi

Shata Ya Shaida Ma Ni Zan Dade A Bisa Kan Karagar Mulki – Sarkin Ningi

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

A ranar Talata 15/2/2021 da ta gabata wakilinmu, Dokta Aliyu...

Matasa Su Dage Da Neman Ilimi Da Koyon Sana’oin Hannu – Dakta Ibrahim Agege 

Matasa Su Dage Da Neman Ilimi Da Koyon Sana’oin Hannu – Dakta Ibrahim Agege 

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai Legas Neman ilmi da koyon sana’oin...

Hajiya Ummi Muhammed Ta Zama Sarauniyar Matan Jihohin Yamma

Hajiya Ummi Muhammed Ta Zama Sarauniyar Matan Jihohin Yamma

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Legas Koda- yaushe cancanta da rashinta...

Next Post
Kasashen Waje

Kwankwaso Ya Yi Farin Ciki Da Dawowar Dalibai 370 Da Ya Tura Karatu Kasashen Waje

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version