• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci INEC Ta Yi Watsi Da ‘Yan Takarar Da Ba Su Shiga Zabukan Fitar Da Gwani Ba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
An Bukaci INEC Ta Yi Watsi Da ‘Yan Takarar Da Ba Su Shiga Zabukan Fitar Da Gwani Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyoyin fararen hula (CSOs) sun bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta yi watsi da kin amincewa da ‘yan takarar da aka mika mata sunayensu ba tare da sun shiga zabukan fitar da gwanaye da aka gudanar a jam’iyyunsu ba.

CSOs din sun kuma jawo jawo hankalin jam’iyyun siyasa da cewa su tabbatar da sun maida sunayen asalin wadanda suka shiga zabukan fitar da gwanaye a maimakon maye sunayensu da wasu da ba su ma shiga zabukan ba.

  • Karancin Kayan Aiki: Ko INEC Za Ta Iya Kammala Sababbin Rijistar Masu Zabe

LEADERSHIP ta labarto cewa, jam’iyyar APC ta gabatar da jerin sunayen wasu ‘yan takarar da ba su ma shiga aka dama da su a zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyar ba.

Kungiyoyin da suka zanta da LEADERSHIP kan wannan batun su ne: Transition Monitoring Group (TMG) Transparency International (TI) da kuma Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC).

Shugaban COS, Awwal Musa Rafsanjani, ya misalta Mika sunayen wadanda ba su shiga zabukan ba a matsayin rashin adalci mafi girma, ya kuma kara da cewa hakan take demokradiyya ne kai tsaye.

Labarai Masu Nasaba

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

“Ta yaya mutumin da bai fita takarar fitar da gwani ba zai kasance dan takarar jam’iyyar a zaben 2023?” Rafsanjani ya tambaya.

“Mutane su na yin hakan ne don rigar mulki da suke da shi, ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan ta tsaya kan gaskiya

“Mutane su shiga takarar zabukan cikin gida. Kawai sai INEC ta zo ta amshi sunan wanda bai shiga takarar ba duk kuwa da cewa Jami’anta sun bi sawun zabukan, wannan karan tsaye wa doka ne,” a cewar CSOs din.

Kes Din Lawan, Akpabio Kai Tsaye Ya Take Dokar Zabe, Cewar SANS

Manyan lauyoyi a Nijeriya sun yi suka kan canza sunayen wasu da suka ci zabukan fitar da gwanaye da wasu da ba su shiga zabukan cikin gida ba, su na masu misalta hakan a matsayin rashin mutunta doka da oda.

Kayode Enitan (SAN) ya shaida cewar akwai bukatar INEC ta ki karban sunan duk wanda bai sjiya zabukan fitar da gwani ba lura da sashin dokar zabe ta 31 da 33.

Ya ce, “A fayyace yake bisa doron doka na canza ‘yan takara bayan zaben fitar da gwani, sashin dokar zabe na 31 da 33 ya bayyana a zahirance cewa ana canza dan takara ne kawai idan wanda ya ci ya janye bisa radin kashin kansa ko ya mutu.”

Ya kara da cewa, “Idan ‘yan takara sun janye bisa kashin kansu ko sun mutu, sabon zaben fitar da gwani jam’iyyar za ta gudanar.

“INEC ba za ta karbi sunan wani da aka canza da bai fito ta hanyar gudanar da sabon zaben fitar da gwani ba bayan mutuwa ko janyewar wanda ya ci da fari.

Machina Ya Ce Zai Dauki Matakin Shari’a Kan Tikitinsa Na Sanatan Yobe Ta Arewa

Kazalika, wanda ya ci zaben fitar da gwani na Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC, Hon Bashir Sheriff Machina, ya bayyana cewar, ya tabbatar jam’iyyar ta mika sunan Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmad Ibrahim Lawan ga INEC a maimakon nashi sunan.

Machina, wanda ya yi magana ta bakin Kakainsa, Hussaini Mohammed Isa, ya ce za su dauki matakin shari’a domin tabbatar da adalci, ya ce ba zai lamunci abun da aka masa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufofin Amurka Kan Kasar Sin Yaudara Ne Munafunci Da Kuma Hadari

Next Post

2023: Da Karfin Kuri’unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

Related

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

43 minutes ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

6 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

7 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

8 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

20 hours ago
Next Post
2023: Da Karfin Kuri’unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

2023: Da Karfin Kuri'unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.