• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci INEC Ta Yi Watsi Da ‘Yan Takarar Da Ba Su Shiga Zabukan Fitar Da Gwani Ba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
An Bukaci INEC Ta Yi Watsi Da ‘Yan Takarar Da Ba Su Shiga Zabukan Fitar Da Gwani Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyoyin fararen hula (CSOs) sun bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta yi watsi da kin amincewa da ‘yan takarar da aka mika mata sunayensu ba tare da sun shiga zabukan fitar da gwanaye da aka gudanar a jam’iyyunsu ba.

CSOs din sun kuma jawo jawo hankalin jam’iyyun siyasa da cewa su tabbatar da sun maida sunayen asalin wadanda suka shiga zabukan fitar da gwanaye a maimakon maye sunayensu da wasu da ba su ma shiga zabukan ba.

  • Karancin Kayan Aiki: Ko INEC Za Ta Iya Kammala Sababbin Rijistar Masu Zabe

LEADERSHIP ta labarto cewa, jam’iyyar APC ta gabatar da jerin sunayen wasu ‘yan takarar da ba su ma shiga aka dama da su a zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyar ba.

Kungiyoyin da suka zanta da LEADERSHIP kan wannan batun su ne: Transition Monitoring Group (TMG) Transparency International (TI) da kuma Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC).

Shugaban COS, Awwal Musa Rafsanjani, ya misalta Mika sunayen wadanda ba su shiga zabukan ba a matsayin rashin adalci mafi girma, ya kuma kara da cewa hakan take demokradiyya ne kai tsaye.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

“Ta yaya mutumin da bai fita takarar fitar da gwani ba zai kasance dan takarar jam’iyyar a zaben 2023?” Rafsanjani ya tambaya.

“Mutane su na yin hakan ne don rigar mulki da suke da shi, ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan ta tsaya kan gaskiya

“Mutane su shiga takarar zabukan cikin gida. Kawai sai INEC ta zo ta amshi sunan wanda bai shiga takarar ba duk kuwa da cewa Jami’anta sun bi sawun zabukan, wannan karan tsaye wa doka ne,” a cewar CSOs din.

Kes Din Lawan, Akpabio Kai Tsaye Ya Take Dokar Zabe, Cewar SANS

Manyan lauyoyi a Nijeriya sun yi suka kan canza sunayen wasu da suka ci zabukan fitar da gwanaye da wasu da ba su shiga zabukan cikin gida ba, su na masu misalta hakan a matsayin rashin mutunta doka da oda.

Kayode Enitan (SAN) ya shaida cewar akwai bukatar INEC ta ki karban sunan duk wanda bai sjiya zabukan fitar da gwani ba lura da sashin dokar zabe ta 31 da 33.

Ya ce, “A fayyace yake bisa doron doka na canza ‘yan takara bayan zaben fitar da gwani, sashin dokar zabe na 31 da 33 ya bayyana a zahirance cewa ana canza dan takara ne kawai idan wanda ya ci ya janye bisa radin kashin kansa ko ya mutu.”

Ya kara da cewa, “Idan ‘yan takara sun janye bisa kashin kansu ko sun mutu, sabon zaben fitar da gwani jam’iyyar za ta gudanar.

“INEC ba za ta karbi sunan wani da aka canza da bai fito ta hanyar gudanar da sabon zaben fitar da gwani ba bayan mutuwa ko janyewar wanda ya ci da fari.

Machina Ya Ce Zai Dauki Matakin Shari’a Kan Tikitinsa Na Sanatan Yobe Ta Arewa

Kazalika, wanda ya ci zaben fitar da gwani na Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC, Hon Bashir Sheriff Machina, ya bayyana cewar, ya tabbatar jam’iyyar ta mika sunan Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmad Ibrahim Lawan ga INEC a maimakon nashi sunan.

Machina, wanda ya yi magana ta bakin Kakainsa, Hussaini Mohammed Isa, ya ce za su dauki matakin shari’a domin tabbatar da adalci, ya ce ba zai lamunci abun da aka masa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufofin Amurka Kan Kasar Sin Yaudara Ne Munafunci Da Kuma Hadari

Next Post

2023: Da Karfin Kuri’unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

Related

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa
Labarai

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

16 minutes ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

45 minutes ago
Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
Labarai

Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

2 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

5 hours ago
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

6 hours ago
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Manyan Labarai

Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu

9 hours ago
Next Post
2023: Da Karfin Kuri’unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

2023: Da Karfin Kuri'unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

July 23, 2025
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

July 23, 2025
Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

July 23, 2025
Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

July 23, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

July 23, 2025
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

July 23, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu

July 23, 2025
Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

July 23, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu

July 23, 2025
Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.