ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci INEC Ta Yi Watsi Da ‘Yan Takarar Da Ba Su Shiga Zabukan Fitar Da Gwani Ba

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Inec

Kungiyoyin fararen hula (CSOs) sun bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta yi watsi da kin amincewa da ‘yan takarar da aka mika mata sunayensu ba tare da sun shiga zabukan fitar da gwanaye da aka gudanar a jam’iyyunsu ba.

CSOs din sun kuma jawo jawo hankalin jam’iyyun siyasa da cewa su tabbatar da sun maida sunayen asalin wadanda suka shiga zabukan fitar da gwanaye a maimakon maye sunayensu da wasu da ba su ma shiga zabukan ba.

  • Karancin Kayan Aiki: Ko INEC Za Ta Iya Kammala Sababbin Rijistar Masu Zabe

LEADERSHIP ta labarto cewa, jam’iyyar APC ta gabatar da jerin sunayen wasu ‘yan takarar da ba su ma shiga aka dama da su a zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyar ba.

ADVERTISEMENT

Kungiyoyin da suka zanta da LEADERSHIP kan wannan batun su ne: Transition Monitoring Group (TMG) Transparency International (TI) da kuma Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC).

Shugaban COS, Awwal Musa Rafsanjani, ya misalta Mika sunayen wadanda ba su shiga zabukan ba a matsayin rashin adalci mafi girma, ya kuma kara da cewa hakan take demokradiyya ne kai tsaye.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Ta yaya mutumin da bai fita takarar fitar da gwani ba zai kasance dan takarar jam’iyyar a zaben 2023?” Rafsanjani ya tambaya.

“Mutane su na yin hakan ne don rigar mulki da suke da shi, ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan ta tsaya kan gaskiya

“Mutane su shiga takarar zabukan cikin gida. Kawai sai INEC ta zo ta amshi sunan wanda bai shiga takarar ba duk kuwa da cewa Jami’anta sun bi sawun zabukan, wannan karan tsaye wa doka ne,” a cewar CSOs din.

Kes Din Lawan, Akpabio Kai Tsaye Ya Take Dokar Zabe, Cewar SANS

Manyan lauyoyi a Nijeriya sun yi suka kan canza sunayen wasu da suka ci zabukan fitar da gwanaye da wasu da ba su shiga zabukan cikin gida ba, su na masu misalta hakan a matsayin rashin mutunta doka da oda.

Kayode Enitan (SAN) ya shaida cewar akwai bukatar INEC ta ki karban sunan duk wanda bai sjiya zabukan fitar da gwani ba lura da sashin dokar zabe ta 31 da 33.

Ya ce, “A fayyace yake bisa doron doka na canza ‘yan takara bayan zaben fitar da gwani, sashin dokar zabe na 31 da 33 ya bayyana a zahirance cewa ana canza dan takara ne kawai idan wanda ya ci ya janye bisa radin kashin kansa ko ya mutu.”

Ya kara da cewa, “Idan ‘yan takara sun janye bisa kashin kansu ko sun mutu, sabon zaben fitar da gwani jam’iyyar za ta gudanar.

“INEC ba za ta karbi sunan wani da aka canza da bai fito ta hanyar gudanar da sabon zaben fitar da gwani ba bayan mutuwa ko janyewar wanda ya ci da fari.

Machina Ya Ce Zai Dauki Matakin Shari’a Kan Tikitinsa Na Sanatan Yobe Ta Arewa

Kazalika, wanda ya ci zaben fitar da gwani na Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC, Hon Bashir Sheriff Machina, ya bayyana cewar, ya tabbatar jam’iyyar ta mika sunan Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmad Ibrahim Lawan ga INEC a maimakon nashi sunan.

Machina, wanda ya yi magana ta bakin Kakainsa, Hussaini Mohammed Isa, ya ce za su dauki matakin shari’a domin tabbatar da adalci, ya ce ba zai lamunci abun da aka masa ba.

Inec
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
2023: Da Karfin Kuri’unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

2023: Da Karfin Kuri'unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.