ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci INEC Ta Yi Watsi Da ‘Yan Takarar Da Ba Su Shiga Zabukan Fitar Da Gwani Ba

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Inec

Kungiyoyin fararen hula (CSOs) sun bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta yi watsi da kin amincewa da ‘yan takarar da aka mika mata sunayensu ba tare da sun shiga zabukan fitar da gwanaye da aka gudanar a jam’iyyunsu ba.

CSOs din sun kuma jawo jawo hankalin jam’iyyun siyasa da cewa su tabbatar da sun maida sunayen asalin wadanda suka shiga zabukan fitar da gwanaye a maimakon maye sunayensu da wasu da ba su ma shiga zabukan ba.

  • Karancin Kayan Aiki: Ko INEC Za Ta Iya Kammala Sababbin Rijistar Masu Zabe

LEADERSHIP ta labarto cewa, jam’iyyar APC ta gabatar da jerin sunayen wasu ‘yan takarar da ba su ma shiga aka dama da su a zabukan fitar da gwanaye na jam’iyyar ba.

ADVERTISEMENT

Kungiyoyin da suka zanta da LEADERSHIP kan wannan batun su ne: Transition Monitoring Group (TMG) Transparency International (TI) da kuma Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC).

Shugaban COS, Awwal Musa Rafsanjani, ya misalta Mika sunayen wadanda ba su shiga zabukan ba a matsayin rashin adalci mafi girma, ya kuma kara da cewa hakan take demokradiyya ne kai tsaye.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Ta yaya mutumin da bai fita takarar fitar da gwani ba zai kasance dan takarar jam’iyyar a zaben 2023?” Rafsanjani ya tambaya.

“Mutane su na yin hakan ne don rigar mulki da suke da shi, ya kamata INEC ta yi watsi da irin wannan ta tsaya kan gaskiya

“Mutane su shiga takarar zabukan cikin gida. Kawai sai INEC ta zo ta amshi sunan wanda bai shiga takarar ba duk kuwa da cewa Jami’anta sun bi sawun zabukan, wannan karan tsaye wa doka ne,” a cewar CSOs din.

Kes Din Lawan, Akpabio Kai Tsaye Ya Take Dokar Zabe, Cewar SANS

Manyan lauyoyi a Nijeriya sun yi suka kan canza sunayen wasu da suka ci zabukan fitar da gwanaye da wasu da ba su shiga zabukan cikin gida ba, su na masu misalta hakan a matsayin rashin mutunta doka da oda.

Kayode Enitan (SAN) ya shaida cewar akwai bukatar INEC ta ki karban sunan duk wanda bai sjiya zabukan fitar da gwani ba lura da sashin dokar zabe ta 31 da 33.

Ya ce, “A fayyace yake bisa doron doka na canza ‘yan takara bayan zaben fitar da gwani, sashin dokar zabe na 31 da 33 ya bayyana a zahirance cewa ana canza dan takara ne kawai idan wanda ya ci ya janye bisa radin kashin kansa ko ya mutu.”

Ya kara da cewa, “Idan ‘yan takara sun janye bisa kashin kansu ko sun mutu, sabon zaben fitar da gwani jam’iyyar za ta gudanar.

“INEC ba za ta karbi sunan wani da aka canza da bai fito ta hanyar gudanar da sabon zaben fitar da gwani ba bayan mutuwa ko janyewar wanda ya ci da fari.

Machina Ya Ce Zai Dauki Matakin Shari’a Kan Tikitinsa Na Sanatan Yobe Ta Arewa

Kazalika, wanda ya ci zaben fitar da gwani na Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC, Hon Bashir Sheriff Machina, ya bayyana cewar, ya tabbatar jam’iyyar ta mika sunan Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmad Ibrahim Lawan ga INEC a maimakon nashi sunan.

Machina, wanda ya yi magana ta bakin Kakainsa, Hussaini Mohammed Isa, ya ce za su dauki matakin shari’a domin tabbatar da adalci, ya ce ba zai lamunci abun da aka masa ba.

Inec
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
2023: Da Karfin Kuri’unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

2023: Da Karfin Kuri'unku Zaku Sauya Shugabanninku A Zabe Mai Zuwa —Sheikh Gumi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.