ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Daliban Da Suka Lakada Wa Malaminsu Duka A Jihar Ogun

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
Ogun

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Ogun, ta tabbatar da cafke wasu daliban makarantar sakandaren Comprehensive High School da ke karamar hukumar Ilisan-Remo, Ikenne a cikin jihar kan lakada wa Malaminsu duka.

Kakakin rundunar ‘yansandan jiha,  Omolola Odutola ne ya tabbatar da afkuwar lamarin a garin Abeokuta.

  1. Muhimman Abubuwan Da Takardar Karin Kudin Makarantar Sakandaren Gwamnatin Tarayya Ta Kunsa

Lamarin ya afku ne a ranar Talatar da ta gabata inda gungun daliban su goma, aka zarge su da dukan malamin mai suna Kolawole Shonuga sabida ya kama daya daga cikinsu yana magudin jarrabawa da suke kan zanawa a makarantar.

ADVERTISEMENT

Hakan ne ya harzika dalibin mai shekaru 18 da sauran tsagerun abokansa dalibai, inda suka yi wa Malamin kwanton bauna akan hanyarsa bayan tashi daga makaranta, suka lakada masa duka.

‘Yan sanda na ofishin gundumar Remo ne, suka kawo wa malamin dauki, inda suka kamo dalibai goma da ake zargi da aikata laifin.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Tuni dai, an gurfanar da su a gaban kotu bisa wannan ta’asar da suka aikata.

Shugaban kungiyar malaman makarantun sakandare reshen jihar (ASUSS), Felix Agbesanwa ya bukaci abi wa malaman hakkinsa kan cin zarafin da daliban suka yi masa, inda kuma ya nuna damuwarsa akan rayuwar malaman jihar.

Agbesanwa ya kuma jaddada cewa, dole ne daliban da ake zargin, su fuskanci hukunci domin hakan ya zama izina ga sauran daliban da za su yi tunanin aikata irin wannan dabbancin a nan gaba.

Gwamnatin jihar ta bakin mai bata shawara ta mussaman kan ilimi, kimiyya da fasaha Farfesa Abayomi Arigbabu ta yi tir da aikata ta’asar da daliban suka yi, inda ta gargadi Iyayen dalibai a jihar da su tabbatar da suna sa ido kan tarbiyar ‘ya’ayansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Next Post
Cire Tallafin Fetur: Ma’aikata A Jihar Kwara Sun Samu Karin Naira 10,000 Kan Albashinsu

Cire Tallafin Fetur: Ma'aikata A Jihar Kwara Sun Samu Karin Naira 10,000 Kan Albashinsu

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.