ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

by Rabi'u Ali Indabawa
6 seconds ago
Edo

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Edo ta kama wani mutum mai shekaru 49 bisa zargin kashe dansa mai shekaru 15 da kuma binne gawar a asirce a cikin harabar gidansu a Unguwar Uhe, Karamar Hukumar Igueben ta Jihar Edo.

Kakakin rundunar, Eno Ikoedem, ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, inda ta ce lamarin ya faru ne a ranar 5 ga Disamba.

  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • Yadda Ake Funkason Fulawa

Ta ce daga bisani an tono gawar domin ci gaba da bincike bayan mahaifiyar wanda ake zargi, wadda ita ce kakar marigayin, ta ba ‘yansanda bayanai masu amfani.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce, “Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Edo ta kama wani mutum mai shekaru 49 bisa zargin kisan dansa mai shekaru 15 da kuma binne gawarsa a asirce a cikin harabar gidansu a Unguwar Uhe, Karamar Hukumar Igueben ta Jihar Edo.”

“Ranar 6 ga Disamba, 2025, bisa sahihan bayanai, jami’an tsaro karkashin jagorancin Dibisional Police Officer suka tafi wurin da abin ya faru, inda aka tabbatar da sahihancin bayanan.

LABARAI MASU NASABA

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane

“Binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargi ya daki dansa da sanda a ranar Juma’a, 5 ga Disamba, 2025, da misalin karfe 7:00 na yamma, lamarin da ya jawo mutuwar yaron.

“Bayan haka, wanda ake zargin ya haka kabari a cikin harabar gidan ya binne gawar. Kakar marigayin, wadda ita ce mahaifiyar wanda ake zargi mai shekaru 82 da ke zaune a gidan, ta ba ‘yansanda bayanai masu amfani.

“Bayan kammala ka’idojin gudanarwa da suka dace, an tono kabarin, an dauki hotuna, sannan an kwato sandar da ake zargin an yi amfani da ita wajen aikata laifin a matsayin hujja. An kama wanda ake zargi kuma yana hannun hukuma yayin da bincike ke gudana.”

Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Edo, Monday Agbonika, ya umarci a mika shari’ar zuwa Sashen Kisan Kai na Sashen Binciken Laifuka na Jihar domin cikakken bincike da gurfanarwa a gaban kotu.

Ya yi gargadi kan dukkan nau’o’in tashin hankali tare da rokon mazauna yankin da su rika gaggauta kai rahoton duk wani abin da ake zargi zuwa ofishin ‘yansanda mafi kusa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

December 20, 2025
An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane
Kotu Da Ɗansanda

An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane

December 20, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
Kotu Da Ɗansanda

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.