• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ceto Matafiya 21 A Kogi Sa’o’i 48 Bayan Sace Su

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
An Ceto Mutum 3 Bayan Musayar Wuta Da ‘Yan Bindiga A Jihar Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an tsaro a Jihar Kogi sun ceto mutane 21 da aka yi garkuwa da su, sa’o’i 48 bayan sace su a ranar a hanyar Ajaokuta zuwa Itobe a jihar.

Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, wanda ya yaba da kokarin jami’an tsaron, ya jaddada cewa ba za’a iya ci gaba da jure aikata miyagun laifuka a jihar ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya ruwaito.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar
  • Tsohuwar Ministar Jin Kai, Sadiya Ba Ta Ƙi Amsa Gayyatarmu Ba – EFCC

Wata sanarwa da mai taimaka wa gwamnan kan harkokin yada labarai, Onogwu Muhammed ya fitar, ta ce tawagar hadin gwiwa ta jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da ‘yan banga na yankin ne suka yi nasarar ceton.

Wadanda abin ya shafa, galibi matafiya ne, aka shiga da su wani dajin da ba a san ko ina ba a cikin dajin da ke kusa da Karamar Hukumar Ajaokuta ta Jihar Kogi.

Amma Bello da ya samu rahoton faruwar lamarin, ya ba da umarni ga jami’an tsaro da ’yan banga da su gaggauta daukar matakin kubutar da wadanda aka yi garkuwar da su tare da kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

“Wannan karbar umarni da suka yi ya nuna jajircewar Bello wajen tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan kasa/mazaunan da ke karkashinsa.

“Kokarin jami’an tsaron hadin gwiwar ya samar da sakamako cikin mai kyau sa’o’i 48, wanda ya kai ga nasarar ceto mutaum 21 da aka kama.

“Bugu da kari, aikin ya kai ga cafke wasu daga cikin masu garkuwa da mutane yayin da ake ci gaba da gano wadanda ke hannunsu,” in ji sanarwar.

Bello, wanda ya yaba wa jami’an tsaro bisa gaggauwa da daukar matakan da suka dace, ya kuma jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da tsaro a Jihar Kogi.

“Wannan gwamnatin ta himmatu wajen ganin ta bar wata hanya da za ta bi wajen ganin Jihar Kogi ta kasance daya daga cikin jihohin kasar nan mafi aminci.

“Ya yi amfani da damar da ya samu wajen yin gargadi ga masu mugun nufi, ya kuma gargadi masu aikata laifuka kan yin hijira zuwa Kogi domin aikata miyagun laifuka.

“Wannan ya faru ne saboda Kogi wuri ne da ba za a iya shiga a aikata kowane irin laifi ba, don haka wannan gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron jihar.

“Nasarar da aka yi ta wannan ceto ta zo ne a matsayin shaida ga hadin kai da yunkurin da jami’an tsaro ke yi a Jihar Kogi a karkashin jagorancin Bello,” in ji ta.

Ya kara da cewa sadaukar da kai na kare lafiyar ‘yan kasa, tare da tsayuwar daka wajen yaki da masu aikata laifuka, ya nuna irin sadaukarwar da gwamnati ta yi wajen samar da yanayin da mazauna yankin za su iya rayuwa ba tare da tsoro ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Masu GarkuwaSokotoYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda

Next Post

“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

11 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

14 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

16 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

17 hours ago
Next Post
“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

"Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023"

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Kogi

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.