• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ceto Matafiya 21 A Kogi Sa’o’i 48 Bayan Sace Su

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
An Ceto Mutum 3 Bayan Musayar Wuta Da ‘Yan Bindiga A Jihar Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an tsaro a Jihar Kogi sun ceto mutane 21 da aka yi garkuwa da su, sa’o’i 48 bayan sace su a ranar a hanyar Ajaokuta zuwa Itobe a jihar.

Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, wanda ya yaba da kokarin jami’an tsaron, ya jaddada cewa ba za’a iya ci gaba da jure aikata miyagun laifuka a jihar ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya ruwaito.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar
  • Tsohuwar Ministar Jin Kai, Sadiya Ba Ta Ƙi Amsa Gayyatarmu Ba – EFCC

Wata sanarwa da mai taimaka wa gwamnan kan harkokin yada labarai, Onogwu Muhammed ya fitar, ta ce tawagar hadin gwiwa ta jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da ‘yan banga na yankin ne suka yi nasarar ceton.

Wadanda abin ya shafa, galibi matafiya ne, aka shiga da su wani dajin da ba a san ko ina ba a cikin dajin da ke kusa da Karamar Hukumar Ajaokuta ta Jihar Kogi.

Amma Bello da ya samu rahoton faruwar lamarin, ya ba da umarni ga jami’an tsaro da ’yan banga da su gaggauta daukar matakin kubutar da wadanda aka yi garkuwar da su tare da kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Labarai Masu Nasaba

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

“Wannan karbar umarni da suka yi ya nuna jajircewar Bello wajen tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan kasa/mazaunan da ke karkashinsa.

“Kokarin jami’an tsaron hadin gwiwar ya samar da sakamako cikin mai kyau sa’o’i 48, wanda ya kai ga nasarar ceto mutaum 21 da aka kama.

“Bugu da kari, aikin ya kai ga cafke wasu daga cikin masu garkuwa da mutane yayin da ake ci gaba da gano wadanda ke hannunsu,” in ji sanarwar.

Bello, wanda ya yaba wa jami’an tsaro bisa gaggauwa da daukar matakan da suka dace, ya kuma jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da tsaro a Jihar Kogi.

“Wannan gwamnatin ta himmatu wajen ganin ta bar wata hanya da za ta bi wajen ganin Jihar Kogi ta kasance daya daga cikin jihohin kasar nan mafi aminci.

“Ya yi amfani da damar da ya samu wajen yin gargadi ga masu mugun nufi, ya kuma gargadi masu aikata laifuka kan yin hijira zuwa Kogi domin aikata miyagun laifuka.

“Wannan ya faru ne saboda Kogi wuri ne da ba za a iya shiga a aikata kowane irin laifi ba, don haka wannan gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron jihar.

“Nasarar da aka yi ta wannan ceto ta zo ne a matsayin shaida ga hadin kai da yunkurin da jami’an tsaro ke yi a Jihar Kogi a karkashin jagorancin Bello,” in ji ta.

Ya kara da cewa sadaukar da kai na kare lafiyar ‘yan kasa, tare da tsayuwar daka wajen yaki da masu aikata laifuka, ya nuna irin sadaukarwar da gwamnati ta yi wajen samar da yanayin da mazauna yankin za su iya rayuwa ba tare da tsoro ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Masu GarkuwaSokotoYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda

Next Post

“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

Related

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

31 minutes ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

2 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

10 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

13 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

16 hours ago
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

19 hours ago
Next Post
“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

"Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023"

LABARAI MASU NASABA

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.