• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ceto Mutane 12 Daga Hatsarin Mota, Wasu Sun Kone Kurmus A Ebonyi

by Sadiq
3 months ago
in Labarai
0
An Ceto Mutane 12 Daga Hatsarin Mota, Wasu Sun Kone Kurmus A Ebonyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) a Jihar Ebonyi, ta ce ta ceto mutane 12 da wani hatsarin da ya rutsa da su a kan babbar hanyar Abakaliki zuwa Ogoja a ranar 18 ga watan Fabrairu.

Kwamandan hukumar a Ebonyi, Uche Chukwurah ne, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) a Abakaliki a ranar Talata cewa jami’an hukumar sun kai wadanda aka ceto zuwa asibitin koyarwa na tarayya na Alex Ekwueme Abakaliki.

  • Mutum 17 Sun Tsira Daga Hatsarin Jirgin Ruwa A Legas
  • Mun Shirya Samar Da Tsaro A Lokacin Zabe -Janar Irabor

Kwamandan ta ce hatsarin ya afku ne a makarantar horas da malamai (TTC) da ke karshen titin yayin da wadanda abin ya shafa suka samu raunuka daban-daban.

“Mun kai dauki ranar 19 ga Fabrairu kuma an ba da rahoton cewa wadanda abin ya shafa suna karbar magani yayin da aka sallame wasu,” in ji ta.

Ta ce rundunar ba za ta iya tabbatar da adadin wadanda suka mutu a hatsarin ba sai dai iya wadanda suka jikkata.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

“Hatsarin ya hada da motar bas da wata mota kirar Toyota Sienna kuma mun gano cewa motar ta kone.

“Mutanen motar bas din sun riga sun kone kurmus ta yadda ba za mu iya tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba.

“Ana zargin hatsarin ya faru ne sakamakon gudun wuke kima,” in ji Chukwurah.

Wani ganau da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa NAN cewa motar bas din ta nufi Taraba ne daga Ribas.

“Motar bas din ta kwace ne sakamakon kauce wa mai babur daga nan suka yi karo da motar Sienna.

“Motar bas din ta fashe sannan ta kama da wuta,” in ji shi.

Tags: BasEbonyiFRSCHatsarin MotaKonewaSienna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobara Ta Lalata Kayan N23bn A Wata 3 A Nijeriya —Hukuma

Next Post

Ina Rokon ‘Yan Siyasar Nijeriya Da Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe —Obama

Related

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

44 mins ago
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli
Labarai

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

3 hours ago
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano
Manyan Labarai

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

4 hours ago
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu
Manyan Labarai

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

10 hours ago
Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo
Labarai

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

20 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

1 day ago
Next Post
Ina Rokon ‘Yan Siyasar Nijeriya Da Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe —Obama

Ina Rokon 'Yan Siyasar Nijeriya Da Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe —Obama

LABARAI MASU NASABA

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

June 4, 2023
Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

June 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.