• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Wani Mutum Shekara Bakwai Bisa Laifin Lalata Yarinya ‘Yar Shekara 11

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Saboda Yawan Jima’i
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai shari’a S. M. Shu’aibu na Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, ya yanke wa wani matashi mai suna Nasiru Isa dan shekara 33 hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan yari bisa samunsa da laifin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 11.

Wani mai suna Isa, mazaunin Darmanawa Bayan Gidan Kallo a Karamar Hukumar Tarauni ta jihar, an yanke masa hukumcin aikata laifin lalata.

  • Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha
  • Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya

Alakalin kotun ya ce masu gabatar da kara sun tabbatar wa da mai shari’ar ba tare da wata shakka ba, sannan kotun ta yanke wa wanda ake kara hukuncin daurin shekaru bakwai ba tare da zabin biyan tara ba.

Mai shari’a Shu’aibu ya kuma umurci mai laifin da ya biya tarar Naira miliyan 1 a matsayin diyya.

Tun da farko, hukumar hana fataucin mutane ta kasa reshen Jihar Kano, ta ce Isa ya aikata laifin ne a Unguwar Darmanawa, Karamar Hukumar Tarauni, Jihar Kano a ranar 5 ga Oktoba, 2024.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Lauyan da ya shigar da kara, Abdullahi Babale, ya ce Isa ya yaudari ‘yar makocinsa ‘yar shekara 11 ta hanyar jan ta dakin matarsa inda a nan ne ya yi lalata da ita.

“Isa ya yi lalata da yarinyar a wurare uku.

“Na daya a dakin matarsa sannan kuma biyun a wani gini da ba a kammala ba.

“Wanda aka yanke wa hukuncin ya yaudari yarinyar ne da biredi, gyada da kuma Naira 20 kafin ya yi lalata da ita,” Babale ya shaida wa kotu.

Masu gabatar da kara sun gabatar da abubuwa guda biyu, da suka hada da bayanin ikirari na wanda aka yankewa hukuncin da kuma shaidar wacce aka yi wa ta’asar, ga kotun don tabbatar da gaskiyar lamarin.

A cewar Babale, laifin da aka aikata ya ci karo da sashe na 16 (1) na dokar hana fataucin mutane (Haramci) da tilastawa mutane, ta 2015 kuma laifin yana da hukunci a karkashin sashe na 26 (1) na TIP ACT 2015.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HukunciKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kebbi Ta Kafa Kwamitin Kwato Kuɗaɗen Da Aka Sace A Asusun Marayun Jihar

Next Post

Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

2 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

3 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.