• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bisa al’ada, ana sa ran zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu ya fara nadi mukamai bayan da Babban Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Olukayode Ariwoola ya rantsar da shi a matsayin shugaban kasan Nijeriya.

Akwai akalla nade-naden mukamai guda uku da ya kamata sabon shugaban kasa ya yi nan take, domin ci gaba da tafiyar da harkokin gwamnatisa, yayin da sauran mukaman da za su biyu baya dole ne sai majalisa ta amince da su.

  • Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Mukaman guda uku sun hada da sakataren gwamnatin tarayya, shugaban ma’aikata da kuma mai magana da yawun shugaban kasa.
An dai yi ta ce-ce-kuce kan nade-naden mukamai a kan gwamnatin Tinubu da suka hada da na ministoci tun bayan da zababben shugaban kasar ya lashe zabe a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ana sa ran wasu makusantan Tinubu ne za su samu manyan mukamai a cikin gwamnatinsa, wanda wasu ke ganin cewa ya kamata ya bi cancanta da kwarewa ba la’akari da kusance ba.

Wata majiya da ke kusa da zababben shugaban kasa ta bayyana cewa makusantansa da abokai ne za su mamaye majalisar zartarwarsa.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Tinubu bai fito fili ya bayyana jerin sunayen wadanda zai nada mukamai ba a kowane mataki, walau masu taimaka masa da jami’an fadar shugaban kasa da kuma ministoci.

Masu kamun kafa na neman mukamai a sabuwar gwamnatin Tinubu sun fara kunfar baki tun lokacin da ya fara bayar da mukami a gwamnatinsa.

Shugaban kasa Tinubu ya nada Dele Alake a matsayin mai magana da yawunsa, sa’o’i kadan bayan rantsar da shi.

Alake ya dade tare da Tinubu, inda har ya taba rike mukamin kwamishinan yada labarai da dabaru a karkashin Tinubu da ga 1999 zuwa 2007 a lokacin yana gwamnan Jihar Legas.

Haka kuma shugaban ya nada, Ambasada Kunle Adeleke a matsayin zagin shugaban kasa.

Ya kuma nada shugaban matasan APC na kasa, Olusegun Dada a matsayin mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan kafafen yada labarai na zamani.
Mukaman sun fara aiki nan take.

Rahotanni sun nuna cewa wadanda ake sa ran za su samu manayan mukamai dai sun hada da tsohon shugaban majalisar wakilai, Mista Femi Gbajabiamila da tsohon ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Fashola da kuma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir el-Rufai da Mista James Faleke.

Masana harkokin mulki na ganin cewa tun daga lokacin da sabon shugaban kasa ya fara nada mukamai ake gane kamun dudayin mulkinsa. Sun ce idan ya nada mutanen kwarai, to gwamnatinsa za ta iya samun nasara, idan kuma ya nada akasin haka, to gwamnatinsa babu abin da za ta iya tabukawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Next Post

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

3 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

LABARAI MASU NASABA

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.