• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bisa al’ada, ana sa ran zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu ya fara nadi mukamai bayan da Babban Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Olukayode Ariwoola ya rantsar da shi a matsayin shugaban kasan Nijeriya.

Akwai akalla nade-naden mukamai guda uku da ya kamata sabon shugaban kasa ya yi nan take, domin ci gaba da tafiyar da harkokin gwamnatisa, yayin da sauran mukaman da za su biyu baya dole ne sai majalisa ta amince da su.

  • Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Mukaman guda uku sun hada da sakataren gwamnatin tarayya, shugaban ma’aikata da kuma mai magana da yawun shugaban kasa.
An dai yi ta ce-ce-kuce kan nade-naden mukamai a kan gwamnatin Tinubu da suka hada da na ministoci tun bayan da zababben shugaban kasar ya lashe zabe a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ana sa ran wasu makusantan Tinubu ne za su samu manyan mukamai a cikin gwamnatinsa, wanda wasu ke ganin cewa ya kamata ya bi cancanta da kwarewa ba la’akari da kusance ba.

Wata majiya da ke kusa da zababben shugaban kasa ta bayyana cewa makusantansa da abokai ne za su mamaye majalisar zartarwarsa.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Tinubu bai fito fili ya bayyana jerin sunayen wadanda zai nada mukamai ba a kowane mataki, walau masu taimaka masa da jami’an fadar shugaban kasa da kuma ministoci.

Masu kamun kafa na neman mukamai a sabuwar gwamnatin Tinubu sun fara kunfar baki tun lokacin da ya fara bayar da mukami a gwamnatinsa.

Shugaban kasa Tinubu ya nada Dele Alake a matsayin mai magana da yawunsa, sa’o’i kadan bayan rantsar da shi.

Alake ya dade tare da Tinubu, inda har ya taba rike mukamin kwamishinan yada labarai da dabaru a karkashin Tinubu da ga 1999 zuwa 2007 a lokacin yana gwamnan Jihar Legas.

Haka kuma shugaban ya nada, Ambasada Kunle Adeleke a matsayin zagin shugaban kasa.

Ya kuma nada shugaban matasan APC na kasa, Olusegun Dada a matsayin mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan kafafen yada labarai na zamani.
Mukaman sun fara aiki nan take.

Rahotanni sun nuna cewa wadanda ake sa ran za su samu manayan mukamai dai sun hada da tsohon shugaban majalisar wakilai, Mista Femi Gbajabiamila da tsohon ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Fashola da kuma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir el-Rufai da Mista James Faleke.

Masana harkokin mulki na ganin cewa tun daga lokacin da sabon shugaban kasa ya fara nada mukamai ake gane kamun dudayin mulkinsa. Sun ce idan ya nada mutanen kwarai, to gwamnatinsa za ta iya samun nasara, idan kuma ya nada akasin haka, to gwamnatinsa babu abin da za ta iya tabukawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Next Post

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 minutes ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 week ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 week ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

4 weeks ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

4 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

4 weeks ago
Next Post
Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

LABARAI MASU NASABA

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

May 31, 2025
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

May 30, 2025
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

May 30, 2025
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.