• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bisa al’ada, ana sa ran zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu ya fara nadi mukamai bayan da Babban Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Olukayode Ariwoola ya rantsar da shi a matsayin shugaban kasan Nijeriya.

Akwai akalla nade-naden mukamai guda uku da ya kamata sabon shugaban kasa ya yi nan take, domin ci gaba da tafiyar da harkokin gwamnatisa, yayin da sauran mukaman da za su biyu baya dole ne sai majalisa ta amince da su.

  • Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Mukaman guda uku sun hada da sakataren gwamnatin tarayya, shugaban ma’aikata da kuma mai magana da yawun shugaban kasa.
An dai yi ta ce-ce-kuce kan nade-naden mukamai a kan gwamnatin Tinubu da suka hada da na ministoci tun bayan da zababben shugaban kasar ya lashe zabe a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ana sa ran wasu makusantan Tinubu ne za su samu manyan mukamai a cikin gwamnatinsa, wanda wasu ke ganin cewa ya kamata ya bi cancanta da kwarewa ba la’akari da kusance ba.

Wata majiya da ke kusa da zababben shugaban kasa ta bayyana cewa makusantansa da abokai ne za su mamaye majalisar zartarwarsa.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Tinubu bai fito fili ya bayyana jerin sunayen wadanda zai nada mukamai ba a kowane mataki, walau masu taimaka masa da jami’an fadar shugaban kasa da kuma ministoci.

Masu kamun kafa na neman mukamai a sabuwar gwamnatin Tinubu sun fara kunfar baki tun lokacin da ya fara bayar da mukami a gwamnatinsa.

Shugaban kasa Tinubu ya nada Dele Alake a matsayin mai magana da yawunsa, sa’o’i kadan bayan rantsar da shi.

Alake ya dade tare da Tinubu, inda har ya taba rike mukamin kwamishinan yada labarai da dabaru a karkashin Tinubu da ga 1999 zuwa 2007 a lokacin yana gwamnan Jihar Legas.

Haka kuma shugaban ya nada, Ambasada Kunle Adeleke a matsayin zagin shugaban kasa.

Ya kuma nada shugaban matasan APC na kasa, Olusegun Dada a matsayin mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan kafafen yada labarai na zamani.
Mukaman sun fara aiki nan take.

Rahotanni sun nuna cewa wadanda ake sa ran za su samu manayan mukamai dai sun hada da tsohon shugaban majalisar wakilai, Mista Femi Gbajabiamila da tsohon ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Fashola da kuma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir el-Rufai da Mista James Faleke.

Masana harkokin mulki na ganin cewa tun daga lokacin da sabon shugaban kasa ya fara nada mukamai ake gane kamun dudayin mulkinsa. Sun ce idan ya nada mutanen kwarai, to gwamnatinsa za ta iya samun nasara, idan kuma ya nada akasin haka, to gwamnatinsa babu abin da za ta iya tabukawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Next Post

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.