ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

A bisa al’ada, ana sa ran zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu ya fara nadi mukamai bayan da Babban Alkalin-alkalan Nijeriya, Mai shari’a Olukayode Ariwoola ya rantsar da shi a matsayin shugaban kasan Nijeriya.

Akwai akalla nade-naden mukamai guda uku da ya kamata sabon shugaban kasa ya yi nan take, domin ci gaba da tafiyar da harkokin gwamnatisa, yayin da sauran mukaman da za su biyu baya dole ne sai majalisa ta amince da su.

  • Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Mukaman guda uku sun hada da sakataren gwamnatin tarayya, shugaban ma’aikata da kuma mai magana da yawun shugaban kasa.
An dai yi ta ce-ce-kuce kan nade-naden mukamai a kan gwamnatin Tinubu da suka hada da na ministoci tun bayan da zababben shugaban kasar ya lashe zabe a ranar 25 ga watan Fabrairu.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran wasu makusantan Tinubu ne za su samu manyan mukamai a cikin gwamnatinsa, wanda wasu ke ganin cewa ya kamata ya bi cancanta da kwarewa ba la’akari da kusance ba.

Wata majiya da ke kusa da zababben shugaban kasa ta bayyana cewa makusantansa da abokai ne za su mamaye majalisar zartarwarsa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Tinubu bai fito fili ya bayyana jerin sunayen wadanda zai nada mukamai ba a kowane mataki, walau masu taimaka masa da jami’an fadar shugaban kasa da kuma ministoci.

Masu kamun kafa na neman mukamai a sabuwar gwamnatin Tinubu sun fara kunfar baki tun lokacin da ya fara bayar da mukami a gwamnatinsa.

Shugaban kasa Tinubu ya nada Dele Alake a matsayin mai magana da yawunsa, sa’o’i kadan bayan rantsar da shi.

Alake ya dade tare da Tinubu, inda har ya taba rike mukamin kwamishinan yada labarai da dabaru a karkashin Tinubu da ga 1999 zuwa 2007 a lokacin yana gwamnan Jihar Legas.

Haka kuma shugaban ya nada, Ambasada Kunle Adeleke a matsayin zagin shugaban kasa.

Ya kuma nada shugaban matasan APC na kasa, Olusegun Dada a matsayin mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan kafafen yada labarai na zamani.
Mukaman sun fara aiki nan take.

Rahotanni sun nuna cewa wadanda ake sa ran za su samu manayan mukamai dai sun hada da tsohon shugaban majalisar wakilai, Mista Femi Gbajabiamila da tsohon ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Fashola da kuma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir el-Rufai da Mista James Faleke.

Masana harkokin mulki na ganin cewa tun daga lokacin da sabon shugaban kasa ya fara nada mukamai ake gane kamun dudayin mulkinsa. Sun ce idan ya nada mutanen kwarai, to gwamnatinsa za ta iya samun nasara, idan kuma ya nada akasin haka, to gwamnatinsa babu abin da za ta iya tabukawa.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.