• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Dalilin Faduwar Farashin Doya A Kasuwannin Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
An Gano Dalilin Faduwar Farashin Doya A  Kasuwannin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa, farashin Soya ya fadi kasa war was a wasu kasuwannin da ke a jihar Neja, biyo bayan da manoman na Doyar a jihar suka fara cika kasuwannin jihar da Doyar.

Bisa binciken da aka gudanar a manyan kasuwannin da ke a jihar, musamman a kasuwar sa ke a shalkwatar Paiko da ke a cikin karamar hukumar Paikoro da kuma wanda aka gudanar a kasuwanin Gwari da Gwadabe da ke a garin Minna a cikin jihar ta Neja sun nuna cewa, farashin na Doyar ya fadi kasa war was da kusan kashi 30 a cikin dari.

  • Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira

Daya daga cikin masu sayar da ita a kasuwar Paiko Mohammed Salihu, ya sanar da cewa, Doya kwarya 100 da ake sayar wa akan farashin naira 200,000 a baya, a yanzu ana sayar da ita daga naira 40,000 zuwa naira 70,000, inda ya ce, amma ya danganta da girman da Doyar yake da shi.

Mohammed ya ci gaba da cewa, sai dai, har yanzu akwai manomanta da ba su fara kawo ta su Doyar da suka noma zuwa kasuwanni ba, ganin cewa, a yanzu suna ci gaba da more garabasar girbin Waken Soya da suka noma a kakar noman bana ba domin suna da burin masu saye da za su sayar wa da amfanin akan sabon farashi idan farashin ta ya tashi a daga cikin watan janairun, inda hakan zai kasance dai dai da lokacin da suke shirye-shiyen sake sabon yin shukar ta.

Wasu manoman Doyar musamman wadanda suke a yankunan, Munya, Paikoro, Shiroro, Rafi da kuma na sauran wasu kananan hukumomin da ke a cikin jihar sun bayyana cewa, duk da rashin tsaron da suke fuskanta a yankunan na su, sun samu nasarar yin girbi mai yawan gaske a kakar noman ta bana.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

A wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, wasu manoma da suka tashi daga yankunan Shiroro, Munya, Rafi da Paikoro a lokacin daminar da tawuce saboda kalubalen rashin tsaro a yankunan, zuwa wasu yankunan da ba fuskantar kalubalen na rashin tsaron hakan ya ba su sukunin nomanta da dama, inda hakan ya sa suka samu yin girbi mai yawan gaske.

Shi ma wani mai sayen Doyar a kasuwar Gwadabe da ke a garin Minna Mohammed Musa ya tabbatar da faduwar farashin na Doyar, inda ya ce, a yanzu ya sayi Doyar babba akan naira 3,500, wacce a baya, ya sayi daga naira ar 8,000 zuwa naira 9,000.
Liman Mohammed, wani mai sayen Doyar ya ce, ya sayi Doyar kwaya takwas a ‘yan makwanin da suka shege daga naira 6,000 zuwa naira 12,000, amma a yanzu farashin ta sauka kasa matuka.

Wani mai sayen Doyar Abubakar Yahaya ya bayyana cewa, a yanzu ya sayi duk babbar Doyar duk kwaya daya a farashi daga naira 1,500 zuwa naira 2,000 wacce a baya ake sayar da duk kwaya daya babba daga farashin naira 3,000 zuwa naira 5,000.
Shi kuwa Yakubu Mustapha ya ce, farashin na Doyar ya karye ne saboda sabuwar ta da aka cike kasuwanin da ita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanonin Duniya Na Ci Gaba Nuna Himma Da Gwazo Wajen Zuba Jari a Kasar Sin

Next Post

Sin Ta Sha Alwashin Kare Hakkokinta A Gabar Da Amurka Ta Sake Kakabawa Karin Kamfanonin Sin Takunkumi

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

8 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

15 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Sin Ta Sha Alwashin Kare Hakkokinta A Gabar Da Amurka Ta Sake Kakabawa Karin Kamfanonin Sin Takunkumi

Sin Ta Sha Alwashin Kare Hakkokinta A Gabar Da Amurka Ta Sake Kakabawa Karin Kamfanonin Sin Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.