ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira

by Abubakar Abba
4 years ago
Doya

Al’ummar da ke yankin Mumuye a jihar Taraba, akasarinsu manoman doya ne kuma ta nan ne suke samun kudin biyan bukatunsu na yau da kullum.

A karamar hukumar Yorro da Zing an san al’ummar Mumuye wajen noman doya saboda haka suka kasance a kan gaba wajen noman doya a jihar.

  • Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

Sai dai, babban kalubalen da suke fama da shi, shi ne na rashin hanya mai kyau da za su dinga yin safarar doyar da suka noma zuwa kasuwani, musamman kasuwannin da ke makwabtaka da jihar, inda ‘yan na-kama ke yin amfani da wannan damar wajen sayen doyar da suka hake da araha.

ADVERTISEMENT

A dukkan kananan hukumomin biyu, babu wata shinfidaddiyar kwalata da gwamnatin jihar ta yi, musamman babbar hanyar da za ta sada sauran kauyukan da ke a yankunan.
Hanya daya da ta hada shalkwatar Pantisawa da ke a karamar hukumar Yorro da babbar hanyar Jalingo zuwa Yola, gwamnatin jihar Filato ce ta bayar da kwangilar ta, har yanzu ba a kammala ta ba.

Har ila yau, aikin babbar hanya daga Zing zuwa Monkin wanda aikin mazaba ne da mariganyiya Sanata Jummai Ai’sha Alhassan ta faro shi, sima an yi wasti da aikin.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Wata mace mai noman doya a yankin Nyadadi Gorko da ke a Yorro Zulai Muhammed ta koka ne a kan rashin hanya a daukacin yankin na Mumuye, inda ta kara da cewa, ba wani talafa da suke samu daga gun gwamnati kamar yadda gwamnatin ta ke yi wa manoman shinkafa da masara da kuma sauran manoman da ke noma sauran amfanain gona.

Zulai ta ci gaba da cerwa, noman doya abu ne mai wuyar gaske, domin aiki ne da ake shafe wata goma sha biyu ana gudanar da shi, da ya hada da, gyran gona, yin shuka da kuma yin girbi.

A cewarta, akasari ana fara gyaran gona ne a cikin watan Satumba, inda kuma ake fara yin shuka daga a watan Disamba, sannan kuma a hake ta a cikin watan Satumba, inda hakan ke nuna cewa, ana shafe shekara daya ne ana yin aikinta.

Zulai ta ce, manomamn doya na yin amfani da takin zamani kala biyu ne da wanda ke sa doyar saurin girma wato NPK da kuma wanda ke sa jijiyar doyar yin girma, inda ta kara da cewa, irin na doya da ake shuka wa yana tsada, inda hakan ke sanya wa sabon shiga cikin fannin bas a samu wata riba kirki.

Shi ma wani manomin na doya a yankin Haruna Hassan ya sanar da cewa, rashin yin kulawar da ta dace a fannin na jawo wa manomanta rashin samun riba mai yawa, wanda ya ce, akasarin manoman doya a yankunan har yanzu suna yin noman na ta hanyar gargakiya ganin cewa, ba a tanadar masu da kayan aiki na zamani ba.

Bugu da kari shi ma wani manomin doya a karamar hukumar Zing Bulus Shamaki ya bayyana cewa, akasarin maomnaon da ke Mumuye na sayar da wani kashi na doyar da suka noma ne domin su samarwa da kansu kuadaden shiga.

Ya sanar da cewa, akwai bukatar manoman na doya, musamman a yankuna da su hada kansu waje daya su kafa kungiya don yin magana da yawu daya a kan matsalolinsu da kuma yadda za su dinga samun rance don kara fadada sana’ar ta su.

Bugu da kari, shi ma wani manomin doya mai suna Yarima Isa Tafida anda ke da gona a Mumuye ya sanar da cewa, ya na nomanta da yawa.

A bisa wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, ana sayar manyan kwaryar doya a kan farashin naira 150,000, inda kuma ake sayar da kanana daga naira 45,000 zuwa naira 100,000.

Doya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.