ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira

by Abubakar Abba
4 years ago
Doya

Al’ummar da ke yankin Mumuye a jihar Taraba, akasarinsu manoman doya ne kuma ta nan ne suke samun kudin biyan bukatunsu na yau da kullum.

A karamar hukumar Yorro da Zing an san al’ummar Mumuye wajen noman doya saboda haka suka kasance a kan gaba wajen noman doya a jihar.

  • Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

Sai dai, babban kalubalen da suke fama da shi, shi ne na rashin hanya mai kyau da za su dinga yin safarar doyar da suka noma zuwa kasuwani, musamman kasuwannin da ke makwabtaka da jihar, inda ‘yan na-kama ke yin amfani da wannan damar wajen sayen doyar da suka hake da araha.

ADVERTISEMENT

A dukkan kananan hukumomin biyu, babu wata shinfidaddiyar kwalata da gwamnatin jihar ta yi, musamman babbar hanyar da za ta sada sauran kauyukan da ke a yankunan.
Hanya daya da ta hada shalkwatar Pantisawa da ke a karamar hukumar Yorro da babbar hanyar Jalingo zuwa Yola, gwamnatin jihar Filato ce ta bayar da kwangilar ta, har yanzu ba a kammala ta ba.

Har ila yau, aikin babbar hanya daga Zing zuwa Monkin wanda aikin mazaba ne da mariganyiya Sanata Jummai Ai’sha Alhassan ta faro shi, sima an yi wasti da aikin.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Wata mace mai noman doya a yankin Nyadadi Gorko da ke a Yorro Zulai Muhammed ta koka ne a kan rashin hanya a daukacin yankin na Mumuye, inda ta kara da cewa, ba wani talafa da suke samu daga gun gwamnati kamar yadda gwamnatin ta ke yi wa manoman shinkafa da masara da kuma sauran manoman da ke noma sauran amfanain gona.

Zulai ta ci gaba da cerwa, noman doya abu ne mai wuyar gaske, domin aiki ne da ake shafe wata goma sha biyu ana gudanar da shi, da ya hada da, gyran gona, yin shuka da kuma yin girbi.

A cewarta, akasari ana fara gyaran gona ne a cikin watan Satumba, inda kuma ake fara yin shuka daga a watan Disamba, sannan kuma a hake ta a cikin watan Satumba, inda hakan ke nuna cewa, ana shafe shekara daya ne ana yin aikinta.

Zulai ta ce, manomamn doya na yin amfani da takin zamani kala biyu ne da wanda ke sa doyar saurin girma wato NPK da kuma wanda ke sa jijiyar doyar yin girma, inda ta kara da cewa, irin na doya da ake shuka wa yana tsada, inda hakan ke sanya wa sabon shiga cikin fannin bas a samu wata riba kirki.

Shi ma wani manomin na doya a yankin Haruna Hassan ya sanar da cewa, rashin yin kulawar da ta dace a fannin na jawo wa manomanta rashin samun riba mai yawa, wanda ya ce, akasarin manoman doya a yankunan har yanzu suna yin noman na ta hanyar gargakiya ganin cewa, ba a tanadar masu da kayan aiki na zamani ba.

Bugu da kari shi ma wani manomin doya a karamar hukumar Zing Bulus Shamaki ya bayyana cewa, akasarin maomnaon da ke Mumuye na sayar da wani kashi na doyar da suka noma ne domin su samarwa da kansu kuadaden shiga.

Ya sanar da cewa, akwai bukatar manoman na doya, musamman a yankuna da su hada kansu waje daya su kafa kungiya don yin magana da yawu daya a kan matsalolinsu da kuma yadda za su dinga samun rance don kara fadada sana’ar ta su.

Bugu da kari, shi ma wani manomin doya mai suna Yarima Isa Tafida anda ke da gona a Mumuye ya sanar da cewa, ya na nomanta da yawa.

A bisa wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, ana sayar manyan kwaryar doya a kan farashin naira 150,000, inda kuma ake sayar da kanana daga naira 45,000 zuwa naira 100,000.

Doya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.