ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira

by Abubakar Abba
4 years ago
Doya

Al’ummar da ke yankin Mumuye a jihar Taraba, akasarinsu manoman doya ne kuma ta nan ne suke samun kudin biyan bukatunsu na yau da kullum.

A karamar hukumar Yorro da Zing an san al’ummar Mumuye wajen noman doya saboda haka suka kasance a kan gaba wajen noman doya a jihar.

  • Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

Sai dai, babban kalubalen da suke fama da shi, shi ne na rashin hanya mai kyau da za su dinga yin safarar doyar da suka noma zuwa kasuwani, musamman kasuwannin da ke makwabtaka da jihar, inda ‘yan na-kama ke yin amfani da wannan damar wajen sayen doyar da suka hake da araha.

ADVERTISEMENT

A dukkan kananan hukumomin biyu, babu wata shinfidaddiyar kwalata da gwamnatin jihar ta yi, musamman babbar hanyar da za ta sada sauran kauyukan da ke a yankunan.
Hanya daya da ta hada shalkwatar Pantisawa da ke a karamar hukumar Yorro da babbar hanyar Jalingo zuwa Yola, gwamnatin jihar Filato ce ta bayar da kwangilar ta, har yanzu ba a kammala ta ba.

Har ila yau, aikin babbar hanya daga Zing zuwa Monkin wanda aikin mazaba ne da mariganyiya Sanata Jummai Ai’sha Alhassan ta faro shi, sima an yi wasti da aikin.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Wata mace mai noman doya a yankin Nyadadi Gorko da ke a Yorro Zulai Muhammed ta koka ne a kan rashin hanya a daukacin yankin na Mumuye, inda ta kara da cewa, ba wani talafa da suke samu daga gun gwamnati kamar yadda gwamnatin ta ke yi wa manoman shinkafa da masara da kuma sauran manoman da ke noma sauran amfanain gona.

Zulai ta ci gaba da cerwa, noman doya abu ne mai wuyar gaske, domin aiki ne da ake shafe wata goma sha biyu ana gudanar da shi, da ya hada da, gyran gona, yin shuka da kuma yin girbi.

A cewarta, akasari ana fara gyaran gona ne a cikin watan Satumba, inda kuma ake fara yin shuka daga a watan Disamba, sannan kuma a hake ta a cikin watan Satumba, inda hakan ke nuna cewa, ana shafe shekara daya ne ana yin aikinta.

Zulai ta ce, manomamn doya na yin amfani da takin zamani kala biyu ne da wanda ke sa doyar saurin girma wato NPK da kuma wanda ke sa jijiyar doyar yin girma, inda ta kara da cewa, irin na doya da ake shuka wa yana tsada, inda hakan ke sanya wa sabon shiga cikin fannin bas a samu wata riba kirki.

Shi ma wani manomin na doya a yankin Haruna Hassan ya sanar da cewa, rashin yin kulawar da ta dace a fannin na jawo wa manomanta rashin samun riba mai yawa, wanda ya ce, akasarin manoman doya a yankunan har yanzu suna yin noman na ta hanyar gargakiya ganin cewa, ba a tanadar masu da kayan aiki na zamani ba.

Bugu da kari shi ma wani manomin doya a karamar hukumar Zing Bulus Shamaki ya bayyana cewa, akasarin maomnaon da ke Mumuye na sayar da wani kashi na doyar da suka noma ne domin su samarwa da kansu kuadaden shiga.

Ya sanar da cewa, akwai bukatar manoman na doya, musamman a yankuna da su hada kansu waje daya su kafa kungiya don yin magana da yawu daya a kan matsalolinsu da kuma yadda za su dinga samun rance don kara fadada sana’ar ta su.

Bugu da kari, shi ma wani manomin doya mai suna Yarima Isa Tafida anda ke da gona a Mumuye ya sanar da cewa, ya na nomanta da yawa.

A bisa wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, ana sayar manyan kwaryar doya a kan farashin naira 150,000, inda kuma ake sayar da kanana daga naira 45,000 zuwa naira 100,000.

Doya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.