ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gudanar Da Taron Manyan Jami’ai Karo Na 16 Na Dandalin FOCAC

by CGTN Hausa
2 years ago
FOCAC

An gudanar da taron manyan jami’ai karo na 16, na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka ko FOCAC a birnin Beijing, fadar mulkin ksar Sin. Yayin taron na jiya Litinin, an nazarci rahoton kasar Sin game da aiwatar da sakamakon taron ministoci na 8, na kasashe mambobin dandalin, tare da musayar ra’ayoyi game da shirin gudanar da sabon taron shekarar dandalin na 2024 dake tafe.

Cikin jawabin da ya gabatar yayin taron, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Deng Li, ya ce Sin a shirye take ta hada gwiwa, da amincewar juna tsakaninta da nahiyar Afirka, tana kuma fatan wanzar da zaman lafiya da daidaito, da musaya, da koyi da juna tsakaninta da sauran sassan wayewar kai, kana ta shirya tunkarar taron na FOCAC na shekarar badi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Karbi ‘Yan Nijeriya 108 Da Suka Makale A Nijar
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Fara Bai Wa Malamai Da Masu Unguwanni Alawus

Deng Li ya ce, ta hanyar aiwatar da matakan yin aiki tare kan turbar zamanintarwa, Sin da kasashen Afirka, za su bude sabon babin samar da ci gaba, da inganta kai tsakanin kasashe masu tasowa.

ADVERTISEMENT

A sasa bangare kuwa, babban mashawarcin shugaban kasar Senegal kan harkokin waje, kuma jagoran hadin gwiwa na taron Oumar Demba Ba, cewa ya yi tun kafuwar dandalin FOCAC, kasashen Afirka da Sin sun ci gaba da bunkasa hadin gwiwarsu bisa abota, da martaba juna, da amincewar juna, da kuma cin moriya tare.

Demba Ba ya kuma godewa kasar Sin bisa yadda ta aiwatar da tarin ayyukan more rayuwa a sassan kasashen Afirka, ta kuma nunawa duniya aniyar samar da gajiya bisa hadin gwiwa, wanda hakan ya haifar da dunkulewa, da daidaito, da managarcin tsarin hadin gwiwa, wanda ke tabbatar da bunkasuwa a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Daga nan sai jami’in ya godewa yadda Sin din ta goyi bayan shigar kungiyar AU cikin kungiyar G20, da irin kyakkyawar rawar da ta taka wajen inganta wakilcin kasashe masu tasowa, da ingiza sauye-sauye a tsarin gudanarwa na kasa da kasa bisa adalci da sanin ya kamata.

Taron na jiya Litinin dai ya hallara kusan manyan baki 300, da jami’ai da wakilai daga Sin, da na kasashen Afirka 53, da mambobin hukumar zartaswar kungiyar AU, da sauran dandaloli, baya ga masu sa ido daga wasu hukumomin kasa da kasa da na shiyyoyi. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
Daga Birnin Sin

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Next Post
Minna

An Kwato Bindiga AK47 Guda 150 A Minna Bayan Artabu

LABARAI MASU NASABA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.