• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

by Sadiq
2 years ago
Mazakuta

Rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya, Abuja ta ce ta gano ba gaskiya ba ne rahoton da wasu mazauna yankin 14 suka yi cewa an sace musu mazakuta ba.

Kwamishinan ‘yansandan babban birnin tarayya, Haruna Garba, ya ce an gano rahoton ba gaskiya ba ne, bayan da aka duba lafiyar wadanda abun ya shafa.

  • Libya Ta Ba Da Umarnin Tsare Jakadiyar Brussels Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa
  • Jami’ar Danfodiyo Ta Musanta Harin ‘Yan Bindiga A Harabar Jami’ar

Garba ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Abuja kan nasarorin da rundunar ta samu a yaki da miyagun laifuka.

Ya kara da cewa mutane 14 da ke da hannu a lamarin a halin yanzu ana ci gaba da bincike a kansu bayan an tabbatar da karyar da suka yi.

“Ana tuhumar su da bayar da bayanan karya da kuma tayar da hankalin jama’a.

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

“Sun yaudari ‘yansanda wajen tunkarar wani harin da aka kai kan sama da mutane 10 da ake zargi a birnin tarayya a cikin ‘yan makonnin da suka gabata.”

Garba ya ce an sanar da ‘yansandan rahotanni sama da 10, galibinsu a kewayen Garshi, Gwagwalada da Kwali da ke cikin babban birnin tarayya Abuja, inda ya ce wasu daga cikin wadannan rahotanni ba su da tushe.

Sai dai shugaban ‘yansandan ya ce ba a samu asarar rai ba a lamarin ba.

“Rundunar ‘yansandan babban birnin tarayya Abuja ta tattara rahotanni sama da 10 da ake zargi da bacewar mazakutar maza a fadin yankin da kuma kara ta’azzara rikicin da matasa masu fusata ke yi.

“Rundunar ‘yansanda ta dauki matakin hana asarar rayuka da dukiyoyi da kuma dawo da doka da oda.

“Mutane 14 da ake zargi da cewa bacewar mazakutar tasu, an kai su asibiti inda likitan ya tabbatar da cewa sassan jikin nasu yana kuma suna aiki.

“Saboda haka, an gurfanar da su gaban kotu da laifin bayar da bayanan karya da kuma tayar da hankalin jama’a,” in ji shi.

Garba ya yi kira ga mazauna yankin da su gargadi ‘ya’yansu da su daina tayar da hankulan jama’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
Labarai

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar
Labarai

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Next Post
An Sace Dalibai Mata 5 A Jami’ar Katsina

An Sace Dalibai Mata 5 A Jami'ar Katsina

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.