ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Libya Ta Ba Da Umarnin Tsare Jakadiyar Brussels Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa

by Sadiq
3 years ago
Libya

Babban mai shigar da kara na Libya ya ba da umarnin a tsare jakadiyar kasar a Brussels a ranar Talata bisa zargin cin hanci da rashawa, jim kadan bayan da gwamnatin Tripoli da kasashen duniya suka amince da sallame ta.

An yi wa Amel Jerry tambayoyi game da “cin zarafin gwamnati da na kudi” da ake zargin an yi amfani da ita don “samun fa’idar haram ta hanyar kwace dukiyar jama’a ba bisa ka’ida ba da kuma cutar da muradun jama’a”, in ji ofishin mai gabatar da kara Al-Seddik al-Sour.

  • ‘Yan Fashin Daji Sun Kashe Kansila A Katsina
  • Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci

Da yake lura da “dacewar shaidar” kan jakadiyar, Al-Sour ya tuhume ta tare da ba da umarnin tsare ta na wucin gadi, in ji ofishin a cikin wata sanarwa, ba tare da bayyana inda ta ke ba.

ADVERTISEMENT

Tun da farko gwamnatin da Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shi a yammacin Libya ta sanar da korar Jerry ba tare da bayar da wani bayani ba.

Kasar Libya mai arzikin man fetur ta fada cikin rikici tun bayan boren da mutanen kasar suka yi a 2011 wanda ya hambarar da gwamnatin shugaba Moamer Gadhafi, kuma cin hanci da rashawa ya yi kamari a cikin cibiyoyin gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Kasar da ke arewacin Afirka ta kasance cikin rarrabuwar kawuna tsakanin gwamnatoci biyu masu gaba da juna, daya a Tripoli da kuma daya a gabashin Libya da ke samun goyon bayan wani babban soji Khalifa Haftar.

Batun cin hanci da rashawa na baya-bayan nan ya barke ne bayan da aka yada wani faifan murya da aka danganta shi da Jerry a shafukan sada zumunta.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin wata mace tana magana wadda aka bayyana a matsayin sakatariyarta, tana mai da’awar cewa tana bukatar “rasitan karya” na sama da Yuro 200,000 (dala $209,000) don maganin cutar kansa ga wani majiyyaci na Libya.

Sakatariyar ta tabbatar da sahihancin faifan bidiyon ga kafafen yada labarai na Libya.

A cikin faifan bidiyon, matar ta ce dole ne a aika da daftarin zuwa ma’aikatar lafiya ta Libya don samun amincewarta na sakin kudaden.

Biyan kudaden jinya ga ‘yan kasar Libya a kasashen waje, daidaitacciyar al’ada ce ga wakilan kasashen duniya na Libya, amma jami’ai a kai a kai suna yin tir da rashin bin ka’ida.

A cewar jaridar Le Soir ta kasar Belgium, ana kuma zargin Jeary da “shakku” wajen mika kudaden al’ummar Libya da ya kai dubunnan daruruwan daloli, zuwa wani kamfani mallakar danta.

Rahotanni daga kasar Belgium na cewa jakadiyar ta koma kasar Libya, sai dai kawo yanzu babu tabbacin hakan.

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.