ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Libya Ta Ba Da Umarnin Tsare Jakadiyar Brussels Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa

by Sadiq
3 years ago
Libya

Babban mai shigar da kara na Libya ya ba da umarnin a tsare jakadiyar kasar a Brussels a ranar Talata bisa zargin cin hanci da rashawa, jim kadan bayan da gwamnatin Tripoli da kasashen duniya suka amince da sallame ta.

An yi wa Amel Jerry tambayoyi game da “cin zarafin gwamnati da na kudi” da ake zargin an yi amfani da ita don “samun fa’idar haram ta hanyar kwace dukiyar jama’a ba bisa ka’ida ba da kuma cutar da muradun jama’a”, in ji ofishin mai gabatar da kara Al-Seddik al-Sour.

  • ‘Yan Fashin Daji Sun Kashe Kansila A Katsina
  • Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci

Da yake lura da “dacewar shaidar” kan jakadiyar, Al-Sour ya tuhume ta tare da ba da umarnin tsare ta na wucin gadi, in ji ofishin a cikin wata sanarwa, ba tare da bayyana inda ta ke ba.

ADVERTISEMENT

Tun da farko gwamnatin da Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shi a yammacin Libya ta sanar da korar Jerry ba tare da bayar da wani bayani ba.

Kasar Libya mai arzikin man fetur ta fada cikin rikici tun bayan boren da mutanen kasar suka yi a 2011 wanda ya hambarar da gwamnatin shugaba Moamer Gadhafi, kuma cin hanci da rashawa ya yi kamari a cikin cibiyoyin gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Kasar da ke arewacin Afirka ta kasance cikin rarrabuwar kawuna tsakanin gwamnatoci biyu masu gaba da juna, daya a Tripoli da kuma daya a gabashin Libya da ke samun goyon bayan wani babban soji Khalifa Haftar.

Batun cin hanci da rashawa na baya-bayan nan ya barke ne bayan da aka yada wani faifan murya da aka danganta shi da Jerry a shafukan sada zumunta.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin wata mace tana magana wadda aka bayyana a matsayin sakatariyarta, tana mai da’awar cewa tana bukatar “rasitan karya” na sama da Yuro 200,000 (dala $209,000) don maganin cutar kansa ga wani majiyyaci na Libya.

Sakatariyar ta tabbatar da sahihancin faifan bidiyon ga kafafen yada labarai na Libya.

A cikin faifan bidiyon, matar ta ce dole ne a aika da daftarin zuwa ma’aikatar lafiya ta Libya don samun amincewarta na sakin kudaden.

Biyan kudaden jinya ga ‘yan kasar Libya a kasashen waje, daidaitacciyar al’ada ce ga wakilan kasashen duniya na Libya, amma jami’ai a kai a kai suna yin tir da rashin bin ka’ida.

A cewar jaridar Le Soir ta kasar Belgium, ana kuma zargin Jeary da “shakku” wajen mika kudaden al’ummar Libya da ya kai dubunnan daruruwan daloli, zuwa wani kamfani mallakar danta.

Rahotanni daga kasar Belgium na cewa jakadiyar ta koma kasar Libya, sai dai kawo yanzu babu tabbacin hakan.

MASU ALAKA

Libya
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Libya
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Libya
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.