• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Tsohon Alkali A Kotu Kan Zargin Lakada Wa Matar Aure Duka

by Abubakar Abba
1 year ago
Kotu

Ofishin ‘yansanda da ke a Tundun Wada a Karamar Hukumar Zariya da ke Jihar Kaduna, ya gurfanar da tsohon Alkalin Kotun Majistari Khadi Muhmmud Shehu, bisa zargin kutsawa cikin gidan wata matar aure, mai suna Sadiya Muhmmad Halliru tare da lakada mata duka.

Tun da farko, an gurfanar da wanda ake zargin ne, a ranar Talatar da ta gabata a gaban kotun Majistari da ke a Zariya.

  • Kwalara: Kwara Ta Rufe Gine-gine 14 Saboda Rashin Banɗaki, Ta Gargaɗi Masu Gidaje
  • Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Dansanda mai gabatar da kara Sufeta Adamu Abubakar ya shaida wa kotu a yayin da ya gabatar da karar wanda ake zargin cewa, laifin da ake zargin tsohon alkalin, ya saba wa sashi na 327 da na 237 da kuma 239 na kudin Final Kod da aka samar a 2017 a Jihar Kaduna.

Ya kara da cewa, tun da farko mijin matar mai suna Garba Adda’u da ke zaune a unguwar Ginar Ganye da ke a cikin Tudun Jukun Zariya ne, ya shigar korafi a kan zargin a caji ofis din ‘yansanda da ke a Tundun Wada rarar 6 na watan Satumbar 2024.

Ya shaida wa kotun cewa, mijin matar ya zargi tsohon alkalin kan shigar masa gida tare da rufe daki da matar ya kuma lakada mata duka ciki har da dukan wasu kannenta biyu, wanda hakan ya sa ta samu raunuka kuma aka kai ta asibiti na matakin farko, don a yi mata magani.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Sai dai, tsohon alkalin a gaban kotun, ya karyata wannan zargin da ake yi masa.

Lauya mai tsayawa alkalin S.M Abubakar ya roki kotun da ta bayar da belin wanda ake zargin.

Amma dansanda mai gabatar da karar, ya bukaci kotun kar ta bayar da belin, inda ya kafa hujjarsa da cewa, mai karar da wanda ake karar, makotan juna ne, kuma bayar da belinsa, zai iya jefa rayuwar mai karar a cikin hatsarin barazana.

Da yake gatabatar da bayani, babban alkalin Kotunn Majistarin Lukuman Sidi, ya bayar da belin tsohon alkalin a kan Naira 50,000 tare da kawo mutum daya da zai tsaya masa, wanda kuma ya mallaki fasfo na kasa da kasa kuma mazauni a yankin da kotun take da zamanta.

Kazalika alkalin ya dage sauraron karar zuwa ranar 8 ga watan Okutobar 2024.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu

Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.