• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Tsohon Alkali A Kotu Kan Zargin Lakada Wa Matar Aure Duka

by Abubakar Abba
10 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin ‘yansanda da ke a Tundun Wada a Karamar Hukumar Zariya da ke Jihar Kaduna, ya gurfanar da tsohon Alkalin Kotun Majistari Khadi Muhmmud Shehu, bisa zargin kutsawa cikin gidan wata matar aure, mai suna Sadiya Muhmmad Halliru tare da lakada mata duka.

Tun da farko, an gurfanar da wanda ake zargin ne, a ranar Talatar da ta gabata a gaban kotun Majistari da ke a Zariya.

  • Kwalara: Kwara Ta Rufe Gine-gine 14 Saboda Rashin Banɗaki, Ta Gargaɗi Masu Gidaje
  • Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Dansanda mai gabatar da kara Sufeta Adamu Abubakar ya shaida wa kotu a yayin da ya gabatar da karar wanda ake zargin cewa, laifin da ake zargin tsohon alkalin, ya saba wa sashi na 327 da na 237 da kuma 239 na kudin Final Kod da aka samar a 2017 a Jihar Kaduna.

Ya kara da cewa, tun da farko mijin matar mai suna Garba Adda’u da ke zaune a unguwar Ginar Ganye da ke a cikin Tudun Jukun Zariya ne, ya shigar korafi a kan zargin a caji ofis din ‘yansanda da ke a Tundun Wada rarar 6 na watan Satumbar 2024.

Ya shaida wa kotun cewa, mijin matar ya zargi tsohon alkalin kan shigar masa gida tare da rufe daki da matar ya kuma lakada mata duka ciki har da dukan wasu kannenta biyu, wanda hakan ya sa ta samu raunuka kuma aka kai ta asibiti na matakin farko, don a yi mata magani.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Sai dai, tsohon alkalin a gaban kotun, ya karyata wannan zargin da ake yi masa.

Lauya mai tsayawa alkalin S.M Abubakar ya roki kotun da ta bayar da belin wanda ake zargin.

Amma dansanda mai gabatar da karar, ya bukaci kotun kar ta bayar da belin, inda ya kafa hujjarsa da cewa, mai karar da wanda ake karar, makotan juna ne, kuma bayar da belinsa, zai iya jefa rayuwar mai karar a cikin hatsarin barazana.

Da yake gatabatar da bayani, babban alkalin Kotunn Majistarin Lukuman Sidi, ya bayar da belin tsohon alkalin a kan Naira 50,000 tare da kawo mutum daya da zai tsaya masa, wanda kuma ya mallaki fasfo na kasa da kasa kuma mazauni a yankin da kotun take da zamanta.

Kazalika alkalin ya dage sauraron karar zuwa ranar 8 ga watan Okutobar 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GurfanaKotuTsohon AlkaliZariya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Shirya Makudan Kudade Don Inganta Matakan Bata Sunan Kasar Sin

Next Post

Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

6 days ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
Next Post
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu

Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.