• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Wani Matashi A Gaban Kotu Kan Zargin Kashe Wata Mata Da ‘Yarta A Kebbi

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
An Gurfanar Da Wani Matashi A Gaban Kotu Kan Zargin Kashe Wata Mata Da ‘Yarta A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gurfanar da wani mutum mai suna Idris Suleiman a gaban wata babbar kotun jihar Kebbi, bisa laifin kashe wata matar aure da diyarta ‘yar shekara hudu a unguwar Kamfanin Labana da ke cikin Birnin Kebbi.

Wanda ake tuhuma dai Idris Suleiman dan asalin Jamhuriyar Nijar ne ke fuskantar tuhuma biyu na aikata laifin kisan kai da ake iya yanke hukuncin kisa a karkashin sashe na 191 (a) na dokar Penal Code na jihar Kebbi 2021.

  • Zargin Yada Luwadi: Saudiyya Ta Hana Sayar Da Kayan Wasa Na Yara Masu Siffanta Jinsin Mutum

Wakilinmu ya tuna cewa wanda ake zargin ya daba wa matar wuka ne har lahira sannan ya bugi kan karamar yarinyar a kan fale-falen dakin mahaifiyar wanda ya yi sanadin mutuwarta ita ma.

Da take gurfanar da wanda ake zargin a gaban mai shari’a Suleiman Ambursa kuma shi ne babban jojin jihar Kebbi, Darakta mai shigar da kara ta ma’aikatar shari’a a Jihar (DPP), Barista A’isha Abbas tare da Barista Zainab Jabbo da kuma Barista Aminu Diri sun shaida wa kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin ne watanin biyu zuwa na uku da suka gabata a cikin hurumin wannan kotun.

Domin tabbatar da aikata laifin , DPP ta kira shaidu shida tare da gabatar da shaidarsu a gaban kotun a karkashin mai shari’a Sulieman Muhammad Ambursa da ke kotu ta daya a Birnin Kebbi.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Bayan gabatar da shaidar shaidun, lauyoyin masu gabatar da kara sun rufe karar nasu.

Lauyoyin da ake kariyar Wanda ake tuhuma a cikin karar mai lamaba KB/HC/27C/2022, Barista Alhassan Salisu-Muhammad, wanda kuma shi ne Shugaban ofishin Lauyoyin masu kare marasa galihu a Jihar Kebbi tare da wasu lauyoyin da suka riga sun hada da; Barista Iliyasu Adamu da Mrs Afu M. A. suka bude nasu kariya kuma sun tabbatar wa da kotun cewa sun kammala ba da kariyar su a gaban kotun.

Haka kuma Lauyoyin da ke kare wadanda ake tuhuma sun kira shaida guda daya (wanda ake tuhuma) don tabbatar da kare su tare da rufe ba da kariyar su nan take.

Daga nan, Lauyoyin masu gabatar da kara da kuma masu kare wanda ake tuhuma sun nemi izinin kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 30 ga watan Yuni, don gabatar da dukkan hujojin su da kuma yin mahawara kan hujojin a gaban kotun.

Alkalin kotun dai, ya dage sauraren karar zuwa ranar 30 ga watan Yuni domin amincewa da rubutaccen hujojin na lauyoyin bangare biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Ta Haihu, ‘Yan Makwanni Ta Sake Samun Juna-biyu Ta Haifi ‘Yan Uku Rigis

Next Post

Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

4 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

6 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

7 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

8 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

11 hours ago
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

Jami'an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.