ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Wani Matashi A Gaban Kotu Kan Zargin Kashe Wata Mata Da ‘Yarta A Kebbi

by Sulaiman
4 years ago
Kebbi

An gurfanar da wani mutum mai suna Idris Suleiman a gaban wata babbar kotun jihar Kebbi, bisa laifin kashe wata matar aure da diyarta ‘yar shekara hudu a unguwar Kamfanin Labana da ke cikin Birnin Kebbi.

Wanda ake tuhuma dai Idris Suleiman dan asalin Jamhuriyar Nijar ne ke fuskantar tuhuma biyu na aikata laifin kisan kai da ake iya yanke hukuncin kisa a karkashin sashe na 191 (a) na dokar Penal Code na jihar Kebbi 2021.

  • Zargin Yada Luwadi: Saudiyya Ta Hana Sayar Da Kayan Wasa Na Yara Masu Siffanta Jinsin Mutum

Wakilinmu ya tuna cewa wanda ake zargin ya daba wa matar wuka ne har lahira sannan ya bugi kan karamar yarinyar a kan fale-falen dakin mahaifiyar wanda ya yi sanadin mutuwarta ita ma.

ADVERTISEMENT

Da take gurfanar da wanda ake zargin a gaban mai shari’a Suleiman Ambursa kuma shi ne babban jojin jihar Kebbi, Darakta mai shigar da kara ta ma’aikatar shari’a a Jihar (DPP), Barista A’isha Abbas tare da Barista Zainab Jabbo da kuma Barista Aminu Diri sun shaida wa kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin ne watanin biyu zuwa na uku da suka gabata a cikin hurumin wannan kotun.

Domin tabbatar da aikata laifin , DPP ta kira shaidu shida tare da gabatar da shaidarsu a gaban kotun a karkashin mai shari’a Sulieman Muhammad Ambursa da ke kotu ta daya a Birnin Kebbi.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Bayan gabatar da shaidar shaidun, lauyoyin masu gabatar da kara sun rufe karar nasu.

Lauyoyin da ake kariyar Wanda ake tuhuma a cikin karar mai lamaba KB/HC/27C/2022, Barista Alhassan Salisu-Muhammad, wanda kuma shi ne Shugaban ofishin Lauyoyin masu kare marasa galihu a Jihar Kebbi tare da wasu lauyoyin da suka riga sun hada da; Barista Iliyasu Adamu da Mrs Afu M. A. suka bude nasu kariya kuma sun tabbatar wa da kotun cewa sun kammala ba da kariyar su a gaban kotun.

Haka kuma Lauyoyin da ke kare wadanda ake tuhuma sun kira shaida guda daya (wanda ake tuhuma) don tabbatar da kare su tare da rufe ba da kariyar su nan take.

Daga nan, Lauyoyin masu gabatar da kara da kuma masu kare wanda ake tuhuma sun nemi izinin kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 30 ga watan Yuni, don gabatar da dukkan hujojin su da kuma yin mahawara kan hujojin a gaban kotun.

Alkalin kotun dai, ya dage sauraren karar zuwa ranar 30 ga watan Yuni domin amincewa da rubutaccen hujojin na lauyoyin bangare biyu.

Kebbi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

Jami'an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.