• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Harbi Mutane 8, 4 Sun Mutu A Zanga-Zanga A Kano

by Sadiq
1 year ago
Kano

Ana fargabar mutane da dama sun mutu, yayin da wasu da dama kuma suka jikkata, sakamakon wani rikici da ya barke tsakanin ‘yan daba da jami’an tsaro a Jihar Kano.

Yankunan da lamarin ya shafa sun hada da Rijiyar Lemo, Kurna zuwa Bachirawa a karamar hukumar Fagge, Kofar Nassarawa a karamar hukumar Birni, da Unguwa Uku a karamar hukumar Tarauni.

  • Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi A Ranar Lahadi
  • Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

A cewar wasu shaidun gani da ido, arangamar ta fara ne a lokacin da wasu matasa suka bijirewa dokar hana fita da aka sanya a jihar tare da fitowa kan tituna, inda suka ci gaba da zanga-zangar da ta rikide zuwa tashin hankali a Kano.

Wani mazaunin Rijiyar Lemo mai suna Abdulkadir Musa ya ce, “Akalla mutane takwas ne aka harbe a yankinmu da suka hada da mata da yara. Yanzu haka wata tsohuwa ta mutu tare da wasu uku, yayin da da dama suka samu munanan raunuka.

“A gaskiya abin da ya faru shi ne, kun san har yanzu dokar hana fita tana nan, don haka mutane suka bijirewa hakan suka fito suna zanga-zanga. A lokacin ne jami’an tsaro suka fara kai farmaki, suna kokarin tarwatsa su, kuma ana cikin haka ne sai da suka yi harbin domin su tarwatsa masu zanga-zangar.”

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Wani mazaunin garin, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya ce ‘yan daban da suka fake da zanga-zangar yunwar, sun yi yunkurin fasa shaguna, ciki har da shagon Rufaida Yoghourt.

Ya ce jami’an tsaro sun tarwatsa ’yan daban, inda daga nan ne suka fara jifan su da duwatsu.

An bayyana cewa wani jami’in ‘yan sanda ya ji rauni a yayin arangamar, ko da yake ba a tantance shi ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Mutanen da harsashi ya rutsa da su yanzu haka suna samun kulawar likitoci a asibitin Salamatu.

Wata mai amfani da shafukan sada zumunta, Aiha K Nass, ta wallafa, “Muna nan muna makokin kakarmu; ‘yan sanda sun harbe yayana Aliyu. Yanzu haka ya mutu.”

Wani mai amfani da shafukan sada zumunta, Omar Khalid Saleh, ya rubuta cewa, “’Yan sanda a Kano sun mayar da zanga-zangar lumana zuwa wani abu daban. Me ya sa ake harbe-harbe da kashe-kashe? Kuna gayyatar matsala. Sun harbe wannan matashi ne, kuma ya mutu nan take a Kofar Nasarawa, cikin birnin Kano. #EndBadGovernance A Nijeriya #KarshenYanSanda.”

Masu zanga-zangar sun fito kan titin Zariya da ke kan Unguwa Uku amma kuma jami’an tsaro sun tarwatsa su.

An jibge karin jami’an tsaro domin dakile zirga-zirga a Kurna Asabe, kusa da Barikin Sojoji na Bukavu.

Kokarin jin ta bakin kakakin ‘yansandan jihar, ya ci tura domin har zuwa lokacin hada wannan rahoto, SP Abudullahi Haruna Kiyawa bai daga waya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Kano

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.