• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Ayyukan Naira Miliyan 873.66 A Jami’ar Tafawa Balewa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Tafawa balewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da bayar da fifiko ga manyan makarantu, musamman domin a rinka yaye daliban da za su samu ilimin zamani mai inganci da zai yi daidai da na fadin duniya.

Tinubu ya sanar a hakan ne a yayin da yake yin jawabi a taron kaddamar da ayyuka shida da suka lashe sama da naira miliyan 873.66 a jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da na kwalejin kimiyya da fasaha ta Tatari Ali dukkan su da ke Jihar Bauchi.

  • Bauchi Ta Mika Ragamar Filin Jirgin Tafawa Balewa Ga Tarayya
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

Gine-ginen da aka kaddamar sun kunshi tsangayar kimiyya da fasaha da kuma sashen tsangayar fasaha da ke a jami’ar ta Abubakar Tafawa Balewa, sai kuma na dakin taro da dakunan yin gwaje-gwajen magunguna a jami’ar Tatari Ali, wadanda aka gina su daga cikin kudin tallafi na asusun hukumar TETFund na shekarar 2021 zuwa shekarar 2022.

Tinubu wanda ministan kula da harkokin kasashen waje, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya wakilce shi a gurin taron ya sanar da cewa, bunkasa fannin ilimin zamani na daya daga cikin ayyukan da gwamnatin tarayya a karkashin shugabancin jam’iyyar APC ta bai wa fifiko.

Shugaban ya kara da cewa, kirkiro da shirin bai wa daliban jama’a rancen kudin karatu da gwamnatin ta yi, ta yi don ta saukaka wa daliban wajen gudanar da karatunsu.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Acewarsa, gwamnatin ta kuma gana da kungiyar dalibai ta manyan makaratu ta kasa (NANS) don tattaunawa a kan jin dadi da walwalar dailban.

Ya ce, wannan na daga cikin kokarin da gwamnatin ke kan ci gaba da yi don magance kalubalen da daliban manyan makartun kasar ke fuskatan da kuma samar da kyakyawan yanayi a tsakanin gwamnatin da kuma kungiyon daliban na manyan makaratun kasar nan.

Kazalika, Tinubu ya sanar da cewa, a kwanan baya gwamnatinsa ta dakatar da umarnin ba aikin yi ba biyan albashi da ta kakaba wa kungiyar malaman jami’o’in kasar nan (ASUU), wanda wannan umarnin, ya ba su damar karbar albashinsu da gwamnatin ta rike saboda yajin aikin da suka yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUATBUTETFund
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Gwamnati Ta Rika Bai Wa Kamfanonin Gida Aiki – Injiniya Isyaku

Next Post

Kano Ta Raba Tallafi Fiye Da Na Tarayya  – Musa Falaki

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

12 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

12 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

13 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

13 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

15 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

16 hours ago
Next Post
Gwamna Yusuf

Kano Ta Raba Tallafi Fiye Da Na Tarayya  - Musa Falaki

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.