• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Cibiyar ‘Yan Jarida Ta Afirka Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

by Muhammad Bashir and Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Jarida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin da ake na bunkasa ayyukan ‘yan jarida masu amfani da harshen Hausa a Nahiyar Afrika, an kaddamar da cibiyar kungiyar a birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Wannan ne karo na farko da aka samar da irin wannan kungiya bisa la’akari da jajircewar da ake yi na ganin an bunkasa harsunan cikin gida musamman Hausa, wanda yake kokarin mamaye sauran harsuna a Nahiyar Afrika.

  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366
  • Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

A yayin kaddamar da cibiyar kungiyar tare da kwarkwaryar zantawa da ‘yan jaridu na kasa da kasa, da sauran wakilai da suka zo daga sassa daban-daban ciki har da Nijeriya, masu ruwa da tsaki a wannan taro sun bayyana muhimmancin wannan kungiya wadda take da manufar aiwatar da aikin jarida nagartacce musamman zaburar da jama’a kan muhimmancin gina al’umma da samar da ci gaba mai dorewa.

 

Maryam Sarki Azbin, wadda ta zama jigo wajen samar da wannan kungiya, ta ce lokaci ya yi da za a rika amfani da harshen cikin gida wajen isar da muhimman sakonni ga al’umma a duk inda suke.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Sarki Azbin ta bukaci ‘yan jarida da su kauce wa abubuwan da suke bata wa aikinsu kima a idon jama’a kamar izgilanci, da maula, da kwadayi, da bambadanci da keta mutuncin masu fada a ji.

Ta kara da cewa, kungiyar ta ‘yan jarida za ta yi dukkan mai yiwa wajen zaburar da ‘yan jaridu kan yadda za su rika amfani da harshen Hausa wajen sanar da mutane abubuwan da za su amfane su a rayuwarsu ta yau da kullum.

A jawabinsa, shugaban hukumar gidan telebijin da radiyo na jamhuriyar Nijar, RTN, Abdoulaye Koulibaly ya bayyana cewa aikin jarida aiki ne da yake bukatar gaskiya da sanin makamar aiki, don haka kuskure ne ‘yan jarida suke yi wajen ba da labarai na shaci-fadi don son abin hannu wasu masu fada a ji, ko kuma nuna bangaranci yayin fitar da labarai.

Koulibali ya ce samar da wannan kungiya wata dama ce da za ta taimaka wajen magance kalubalen da ‘yan jarida suke fuskanta ta fannin gudanar da ayyukansu, musamman wajen amfani da harshe na cikin gida.

Sauran wadanda suka yi jawabi a wurin sun gamsu da tsare-tsare da manufofin da aka gina kungiyar a kan su, musamman tabbatar da hadin kai da mu’amala a tsakanin ‘yan jarida na kasashe 11 da ke Nahiyar Afrika, suna masu cewa yawan da ‘yan jaridar Hausa da ake da su a Nihiyar sun isa su taka gagarumar gudunmawa wajen magance kalubalen da ake fuskanta, da kuma karfafawa masu kwarin giwa wajen ganin sun yi abin da ya dace na kyautata rayuwar al’ummar yankin.

Shi ma a nasa bangaren, ma’aikaci a hukumar telebijin a tarayyar Nijeriya (NTA), Aliyu Rabe Aliyu ya ce, babban aikin da kungiyar ‘yan jarida masu amfani da harshen Hausa za ta sa a gaba shi ne, sauya fasalin aikin jaridar gado na ‘yan ku ci ku ba mu, ya zuwa aikin jarida na samar da mafita ga tulin kalubalen da yankin yake fuskanta ta hanyar amfani da harshen da kowa yake sonsa, kuma yake amfani da shi watau harshen Hausa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

Next Post

‘Yan Nijeriya Miliyan 33 Na Iya Fuskantar Matsalar Rashin Abinci A 2025 —Rahoto

Related

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe
Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

1 hour ago
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano
Labarai

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

4 hours ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

5 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

8 hours ago
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

10 hours ago
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Labarai

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

11 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

‘Yan Nijeriya Miliyan 33 Na Iya Fuskantar Matsalar Rashin Abinci A 2025 —Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.