• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Cibiyar ‘Yan Jarida Ta Afirka Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

by Muhammad Bashir and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Jarida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin da ake na bunkasa ayyukan ‘yan jarida masu amfani da harshen Hausa a Nahiyar Afrika, an kaddamar da cibiyar kungiyar a birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Wannan ne karo na farko da aka samar da irin wannan kungiya bisa la’akari da jajircewar da ake yi na ganin an bunkasa harsunan cikin gida musamman Hausa, wanda yake kokarin mamaye sauran harsuna a Nahiyar Afrika.

  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366
  • Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

A yayin kaddamar da cibiyar kungiyar tare da kwarkwaryar zantawa da ‘yan jaridu na kasa da kasa, da sauran wakilai da suka zo daga sassa daban-daban ciki har da Nijeriya, masu ruwa da tsaki a wannan taro sun bayyana muhimmancin wannan kungiya wadda take da manufar aiwatar da aikin jarida nagartacce musamman zaburar da jama’a kan muhimmancin gina al’umma da samar da ci gaba mai dorewa.

 

Maryam Sarki Azbin, wadda ta zama jigo wajen samar da wannan kungiya, ta ce lokaci ya yi da za a rika amfani da harshen cikin gida wajen isar da muhimman sakonni ga al’umma a duk inda suke.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Sarki Azbin ta bukaci ‘yan jarida da su kauce wa abubuwan da suke bata wa aikinsu kima a idon jama’a kamar izgilanci, da maula, da kwadayi, da bambadanci da keta mutuncin masu fada a ji.

Ta kara da cewa, kungiyar ta ‘yan jarida za ta yi dukkan mai yiwa wajen zaburar da ‘yan jaridu kan yadda za su rika amfani da harshen Hausa wajen sanar da mutane abubuwan da za su amfane su a rayuwarsu ta yau da kullum.

A jawabinsa, shugaban hukumar gidan telebijin da radiyo na jamhuriyar Nijar, RTN, Abdoulaye Koulibaly ya bayyana cewa aikin jarida aiki ne da yake bukatar gaskiya da sanin makamar aiki, don haka kuskure ne ‘yan jarida suke yi wajen ba da labarai na shaci-fadi don son abin hannu wasu masu fada a ji, ko kuma nuna bangaranci yayin fitar da labarai.

Koulibali ya ce samar da wannan kungiya wata dama ce da za ta taimaka wajen magance kalubalen da ‘yan jarida suke fuskanta ta fannin gudanar da ayyukansu, musamman wajen amfani da harshe na cikin gida.

Sauran wadanda suka yi jawabi a wurin sun gamsu da tsare-tsare da manufofin da aka gina kungiyar a kan su, musamman tabbatar da hadin kai da mu’amala a tsakanin ‘yan jarida na kasashe 11 da ke Nahiyar Afrika, suna masu cewa yawan da ‘yan jaridar Hausa da ake da su a Nihiyar sun isa su taka gagarumar gudunmawa wajen magance kalubalen da ake fuskanta, da kuma karfafawa masu kwarin giwa wajen ganin sun yi abin da ya dace na kyautata rayuwar al’ummar yankin.

Shi ma a nasa bangaren, ma’aikaci a hukumar telebijin a tarayyar Nijeriya (NTA), Aliyu Rabe Aliyu ya ce, babban aikin da kungiyar ‘yan jarida masu amfani da harshen Hausa za ta sa a gaba shi ne, sauya fasalin aikin jaridar gado na ‘yan ku ci ku ba mu, ya zuwa aikin jarida na samar da mafita ga tulin kalubalen da yankin yake fuskanta ta hanyar amfani da harshen da kowa yake sonsa, kuma yake amfani da shi watau harshen Hausa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

Next Post

‘Yan Nijeriya Miliyan 33 Na Iya Fuskantar Matsalar Rashin Abinci A 2025 —Rahoto

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

19 minutes ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

3 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

6 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

7 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

‘Yan Nijeriya Miliyan 33 Na Iya Fuskantar Matsalar Rashin Abinci A 2025 —Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.