• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Mutum 89 Da Ake Zargi Da Fashi Da Dillancin Muggan Kwayoyi A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansanda a Jihar Kano, ta ce ta samu gagarumar nasara a kokarinta na tabbatar da tsaron lafiyar jama’a da kuma rigakafin aikata laifuka.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Salman Dogo Garba, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a shalkwatar ‘yansandan da ke Bompal.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas
  • Da Gangan Aka Rikirkita Tsarin Zaben Nijeriya Domin A Samu Damar Yin Magudi – Sanata Ndume

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wakilta, CP, ya ce rundunar ta samu nasarar cafke wasu miyagun mutane 89 da suka hada da ‘yan fashi da makami 15, wasu 10 kuma da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi, da kuma mutum daya da ake zargi da safarar mutane.

 

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Har ila yau, ya bayyana cewa, ‘yansandan sun samu nasarar kubutar da mutum biyu da aka yi garkuwa da su.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yan sandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Bakardin Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

Bugu da kari, ya kara da cewa, matakin da rundunar ta dauka na fara gudanar da ayyukan al’umma masu inganci, sun hada da gudanar da ayyukan leken asiri, da kuma sintiri na gani ba dare ba rana, wanda hakan ya haifar da sakamako mai kyau, inda aka gurfanar da mutane 43 da ake tuhuma a gaban kotu, yayin da wasu 46 ke fuskantar bincike.

 

Kiyawa ya jaddada cewa rundunar ta fahimci muhimmancin hadin kan al’umma da hadin gwiwa wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafofin yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.

 

Ya bukaci mazauna yankin da su bai wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro hadin kai, da kuma shiga cikin aminci a cikin bukukuwan, tare da mutunta ‘yancin wasu.

 

Shugaban ‘yansandan ya kuma jajantawa iyalan ‘yansandan biyar da suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a ranar 23 ga watan Satumba 2024, ya kuma yaba da addu’o’i da goyon bayan da aka bai wa iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka jikkata.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yansandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ayyukan 'Yan BindigaNDLEATa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alakar Arsenal Da ‘Yan Wasa Bakaken Fata

Next Post

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

1 month ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

1 month ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

August 12, 2025
Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

August 12, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

August 12, 2025
Kano

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

August 12, 2025
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.