• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Mutum 89 Da Ake Zargi Da Fashi Da Dillancin Muggan Kwayoyi A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
11 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansanda a Jihar Kano, ta ce ta samu gagarumar nasara a kokarinta na tabbatar da tsaron lafiyar jama’a da kuma rigakafin aikata laifuka.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Salman Dogo Garba, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a shalkwatar ‘yansandan da ke Bompal.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas
  • Da Gangan Aka Rikirkita Tsarin Zaben Nijeriya Domin A Samu Damar Yin Magudi – Sanata Ndume

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wakilta, CP, ya ce rundunar ta samu nasarar cafke wasu miyagun mutane 89 da suka hada da ‘yan fashi da makami 15, wasu 10 kuma da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi, da kuma mutum daya da ake zargi da safarar mutane.

 

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Har ila yau, ya bayyana cewa, ‘yansandan sun samu nasarar kubutar da mutum biyu da aka yi garkuwa da su.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yan sandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Bakardin Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

Bugu da kari, ya kara da cewa, matakin da rundunar ta dauka na fara gudanar da ayyukan al’umma masu inganci, sun hada da gudanar da ayyukan leken asiri, da kuma sintiri na gani ba dare ba rana, wanda hakan ya haifar da sakamako mai kyau, inda aka gurfanar da mutane 43 da ake tuhuma a gaban kotu, yayin da wasu 46 ke fuskantar bincike.

 

Kiyawa ya jaddada cewa rundunar ta fahimci muhimmancin hadin kan al’umma da hadin gwiwa wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafofin yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.

 

Ya bukaci mazauna yankin da su bai wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro hadin kai, da kuma shiga cikin aminci a cikin bukukuwan, tare da mutunta ‘yancin wasu.

 

Shugaban ‘yansandan ya kuma jajantawa iyalan ‘yansandan biyar da suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a ranar 23 ga watan Satumba 2024, ya kuma yaba da addu’o’i da goyon bayan da aka bai wa iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka jikkata.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yansandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ayyukan 'Yan BindigaNDLEATa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alakar Arsenal Da ‘Yan Wasa Bakaken Fata

Next Post

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

2 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

3 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

3 weeks ago
Next Post
Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

LABARAI MASU NASABA

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

September 4, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

September 4, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

September 4, 2025
An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

September 4, 2025
An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

September 4, 2025
Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

September 4, 2025
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

September 4, 2025
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.