ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Mutum 89 Da Ake Zargi Da Fashi Da Dillancin Muggan Kwayoyi A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 years ago
Fashi

Rundunar ‘yansanda a Jihar Kano, ta ce ta samu gagarumar nasara a kokarinta na tabbatar da tsaron lafiyar jama’a da kuma rigakafin aikata laifuka.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Salman Dogo Garba, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a shalkwatar ‘yansandan da ke Bompal.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas
  • Da Gangan Aka Rikirkita Tsarin Zaben Nijeriya Domin A Samu Damar Yin Magudi – Sanata Ndume

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wakilta, CP, ya ce rundunar ta samu nasarar cafke wasu miyagun mutane 89 da suka hada da ‘yan fashi da makami 15, wasu 10 kuma da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi, da kuma mutum daya da ake zargi da safarar mutane.

 

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Har ila yau, ya bayyana cewa, ‘yansandan sun samu nasarar kubutar da mutum biyu da aka yi garkuwa da su.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yan sandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Bakardin Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

Bugu da kari, ya kara da cewa, matakin da rundunar ta dauka na fara gudanar da ayyukan al’umma masu inganci, sun hada da gudanar da ayyukan leken asiri, da kuma sintiri na gani ba dare ba rana, wanda hakan ya haifar da sakamako mai kyau, inda aka gurfanar da mutane 43 da ake tuhuma a gaban kotu, yayin da wasu 46 ke fuskantar bincike.

 

Kiyawa ya jaddada cewa rundunar ta fahimci muhimmancin hadin kan al’umma da hadin gwiwa wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafofin yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.

 

Ya bukaci mazauna yankin da su bai wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro hadin kai, da kuma shiga cikin aminci a cikin bukukuwan, tare da mutunta ‘yancin wasu.

 

Shugaban ‘yansandan ya kuma jajantawa iyalan ‘yansandan biyar da suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a ranar 23 ga watan Satumba 2024, ya kuma yaba da addu’o’i da goyon bayan da aka bai wa iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka jikkata.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yansandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.

Fashi
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Fashi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.