• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Mutum 89 Da Ake Zargi Da Fashi Da Dillancin Muggan Kwayoyi A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
9 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansanda a Jihar Kano, ta ce ta samu gagarumar nasara a kokarinta na tabbatar da tsaron lafiyar jama’a da kuma rigakafin aikata laifuka.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Salman Dogo Garba, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a shalkwatar ‘yansandan da ke Bompal.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas
  • Da Gangan Aka Rikirkita Tsarin Zaben Nijeriya Domin A Samu Damar Yin Magudi – Sanata Ndume

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wakilta, CP, ya ce rundunar ta samu nasarar cafke wasu miyagun mutane 89 da suka hada da ‘yan fashi da makami 15, wasu 10 kuma da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi, da kuma mutum daya da ake zargi da safarar mutane.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Har ila yau, ya bayyana cewa, ‘yansandan sun samu nasarar kubutar da mutum biyu da aka yi garkuwa da su.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yan sandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Bakardin Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

Bugu da kari, ya kara da cewa, matakin da rundunar ta dauka na fara gudanar da ayyukan al’umma masu inganci, sun hada da gudanar da ayyukan leken asiri, da kuma sintiri na gani ba dare ba rana, wanda hakan ya haifar da sakamako mai kyau, inda aka gurfanar da mutane 43 da ake tuhuma a gaban kotu, yayin da wasu 46 ke fuskantar bincike.

 

Kiyawa ya jaddada cewa rundunar ta fahimci muhimmancin hadin kan al’umma da hadin gwiwa wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafofin yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.

 

Ya bukaci mazauna yankin da su bai wa ‘yansanda da sauran jami’an tsaro hadin kai, da kuma shiga cikin aminci a cikin bukukuwan, tare da mutunta ‘yancin wasu.

 

Shugaban ‘yansandan ya kuma jajantawa iyalan ‘yansandan biyar da suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a ranar 23 ga watan Satumba 2024, ya kuma yaba da addu’o’i da goyon bayan da aka bai wa iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka jikkata.

 

Har ila yau, Kiyawa ya bayyana cewa, rundunar ‘yansandan Kano ta samu nasarar kwato miyagun kwayoyi, da muggan makamai, da kuma dukiyoyin da aka sace, da suka hada da kwalabe na Syrup guda 538 da busasshen ganye masu yawa, wadanda ake zargin hemp din Indiya ne.

 

“Mun kasance muna tattaunawa da masu ruwa da tsaki, ciki har da kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da shawarwarin tsaro da kuma jin dadin hadin kai da goyon bayan gwamnatin Jihar Kano, da sauran hukumomin tsaro, da masu bin doka da oda,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ayyukan 'Yan BindigaNDLEATa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alakar Arsenal Da ‘Yan Wasa Bakaken Fata

Next Post

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

7 days ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
Next Post
Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

Gwamnan Akwa Ibom Ya Naɗa Ƴarsa Muƙamin Matar Gwamna

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.