• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Zargi

Hukumar ‘yansanda a Jihar Adamawa ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da hannu wajen kashe wani mai PoS, Abbas Yuguda, a karamar Hukumar Mayo-Belwa ta Jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Yahaya Nguroje, ya bayyana a wata sanarwa cewa Yuguda, yayin da yake dawowa daga sana’arsa, wasu gungun ‘yan fashi ne suka kai masa hari tare da raunata shi, suka bar shi cikin jini.

  • Sallah: ’Yansanda Sun Yi Alƙawarin Tabbatar Da Tsaro A Kano
  • Ƴansanda Sun Kama  Ɓarayin Waya Masu Amfani Da Keke Napep A Adamawa

Nguroje ya kara da cewa, da samun labarin faruwar lamarin, jami’an ‘yansanda suka ziyarci wurin, inda suka samu Yuguda a wannan hali, daga nan suka garzaya da shi wani asibiti mafi kusa, inda ya mutu a lokacin da yake karvar magani.

PPRO ya ce, “Rundunar ‘yansandan Jihar Adamawa ta kaddamar da bincike kan wani mummunan kisan da aka yi wa wani sana’ar POS, Abbas Yuguda, dan shekara 35, wanda aka kai wa hari a karamar Hukumar Mayo-Belwa.

“Al’amarin ya faru ne a ranar 22 ga Maris, 2025, a lokacin da wanda abin ya shafa ke kan hanyarsa ta komawa gida bayan ya tashi daga wurin sana’arsa, wasu gungun mutane dauke da muggan makamai suka kai masa hari tare da yi masa munanan raunuka inda suka bar shi kwance cikin jini.

LABARAI MASU NASABA

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

“Jami’an ‘yansanda da ke ofishin ‘yansanda, Mayo Belwa, sun isa wurin, inda nan take suka garzaya da wanda abin ya shafa zuwa asibitin Cottage, Mayo-Belwa, domin  kokarin ceton ransa, amma abin takaici, an tabbatar da mutuwarsa a lokacin da ya ke karvar magani.”

Kakakin rundunar ‘yansandan ya ce, ya yi saurin shiga tsakanin wanda ake zargin da matasa suka kama shi domin cetonsa daga hannun matsan inda aka garzaya da shi asibiti.

Ya ci gaba da cewa wasu matasa a yankin da lamarin ya faru sun bi sawu inda suka kama daya daga cikin wadanda ake zargin ’yan fashi da makami ne kuma suka damke shi.

Ya gargadi mazauna jihar kan yin yin hukuncin nan na daukar doka a hannunsu tare da bukatar su da su kai rahoton duk wani abu da ya faru ga ‘yansanda.

“A bisa wannan karfi, daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Umar SNU, wasu fusatattun matasa ne suka bi sawun sa, inda suka yi ta kai ruwa rana kafin ‘yan sanda su kubutar da shi, sannan aka garzaya da shi asibiti domin kula da lafiyarsa, inda a yanzu ya taimaka wajen gudanar da bincike.

“Kwamishanan ‘yansanda, Dankombo Morris, ya yi Allah-wadai da wannan ta’addancin da kakkausar murya, sannan ya bayar da umarnin gudanar da sahihin bincike don tabbatar da an gurfanar da wadanda suka aikata laifin gaban kotu.

“Ya kuma gargadi jama’a da su daina daukar doka a hannunsu, ya kuma bukace su da su bar doka a kodayaushe ta yi aikinta, kuma su ci gaba da tafiyar da ayyukansu yadda ya kamata, rundunar ‘yansandan ta bukaci mazauna yankin da su yi taka-tsan-tsan tare da kai rahoto ga ofishin ‘yansanda mafi kusa,” in ji Nguroje.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a watan Disambar 2024 cewa wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun kai hari a unguwar Atan-Ota da ke karamar hukumar Ado-Odo/Ota ta jihar Ogun inda suka kashe wani jami’in tsaro da ke gadin wata karamar mota a yankin yayin da suka tsere da wata babbar mota da aka ajiye a dajin.

Wakilinmu ya samu labari daga wani mazaunin unguwar cewa wata mai sayar da abinci an gano gawarta a daji babu rai, inda aka yi masa fyade tare da daure ta a wata kusurwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
Manyan Labarai

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A 28-03-2025

LABARAI MASU NASABA

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.