ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Zargi

Hukumar ‘yansanda a Jihar Adamawa ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da hannu wajen kashe wani mai PoS, Abbas Yuguda, a karamar Hukumar Mayo-Belwa ta Jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Yahaya Nguroje, ya bayyana a wata sanarwa cewa Yuguda, yayin da yake dawowa daga sana’arsa, wasu gungun ‘yan fashi ne suka kai masa hari tare da raunata shi, suka bar shi cikin jini.

  • Sallah: ’Yansanda Sun Yi Alƙawarin Tabbatar Da Tsaro A Kano
  • Ƴansanda Sun Kama  Ɓarayin Waya Masu Amfani Da Keke Napep A Adamawa

Nguroje ya kara da cewa, da samun labarin faruwar lamarin, jami’an ‘yansanda suka ziyarci wurin, inda suka samu Yuguda a wannan hali, daga nan suka garzaya da shi wani asibiti mafi kusa, inda ya mutu a lokacin da yake karvar magani.

ADVERTISEMENT

PPRO ya ce, “Rundunar ‘yansandan Jihar Adamawa ta kaddamar da bincike kan wani mummunan kisan da aka yi wa wani sana’ar POS, Abbas Yuguda, dan shekara 35, wanda aka kai wa hari a karamar Hukumar Mayo-Belwa.

“Al’amarin ya faru ne a ranar 22 ga Maris, 2025, a lokacin da wanda abin ya shafa ke kan hanyarsa ta komawa gida bayan ya tashi daga wurin sana’arsa, wasu gungun mutane dauke da muggan makamai suka kai masa hari tare da yi masa munanan raunuka inda suka bar shi kwance cikin jini.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Jami’an ‘yansanda da ke ofishin ‘yansanda, Mayo Belwa, sun isa wurin, inda nan take suka garzaya da wanda abin ya shafa zuwa asibitin Cottage, Mayo-Belwa, domin  kokarin ceton ransa, amma abin takaici, an tabbatar da mutuwarsa a lokacin da ya ke karvar magani.”

Kakakin rundunar ‘yansandan ya ce, ya yi saurin shiga tsakanin wanda ake zargin da matasa suka kama shi domin cetonsa daga hannun matsan inda aka garzaya da shi asibiti.

Ya ci gaba da cewa wasu matasa a yankin da lamarin ya faru sun bi sawu inda suka kama daya daga cikin wadanda ake zargin ’yan fashi da makami ne kuma suka damke shi.

Ya gargadi mazauna jihar kan yin yin hukuncin nan na daukar doka a hannunsu tare da bukatar su da su kai rahoton duk wani abu da ya faru ga ‘yansanda.

“A bisa wannan karfi, daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Umar SNU, wasu fusatattun matasa ne suka bi sawun sa, inda suka yi ta kai ruwa rana kafin ‘yan sanda su kubutar da shi, sannan aka garzaya da shi asibiti domin kula da lafiyarsa, inda a yanzu ya taimaka wajen gudanar da bincike.

“Kwamishanan ‘yansanda, Dankombo Morris, ya yi Allah-wadai da wannan ta’addancin da kakkausar murya, sannan ya bayar da umarnin gudanar da sahihin bincike don tabbatar da an gurfanar da wadanda suka aikata laifin gaban kotu.

“Ya kuma gargadi jama’a da su daina daukar doka a hannunsu, ya kuma bukace su da su bar doka a kodayaushe ta yi aikinta, kuma su ci gaba da tafiyar da ayyukansu yadda ya kamata, rundunar ‘yansandan ta bukaci mazauna yankin da su yi taka-tsan-tsan tare da kai rahoto ga ofishin ‘yansanda mafi kusa,” in ji Nguroje.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a watan Disambar 2024 cewa wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun kai hari a unguwar Atan-Ota da ke karamar hukumar Ado-Odo/Ota ta jihar Ogun inda suka kashe wani jami’in tsaro da ke gadin wata karamar mota a yankin yayin da suka tsere da wata babbar mota da aka ajiye a dajin.

Wakilinmu ya samu labari daga wani mazaunin unguwar cewa wata mai sayar da abinci an gano gawarta a daji babu rai, inda aka yi masa fyade tare da daure ta a wata kusurwa.

Zargi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A 28-03-2025

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.