Sagir Abubakar">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Nemi Tsoffin Daliban Makarantar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Kaita Su Farfado Da Ita

by Sagir Abubakar
February 2, 2021
in LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

An roki masu hannu da shuni da kuma ‘yan kungiyar tsoffin dalibai da su bada gudunmuwarsu domin tabbatar da samar da kyakkyawan yanayin koyo da koyarwa a kwalejin ilimi ta Isa Kaita dake Dutsinma.

Shugaban kwalejin Dr. Maigari Bello Abdu ya bayyana haka ga ‘yan kungiyar kwamitin tuntuba na garin Dutsinma karkashin jagoraincin Bello.
Kamar yadda yace karancin ajujuwa. Ababen zama, dakunan gwaje-gwaje, masallaci da kuma dakin kwanan dalibai na maza na daga cikin manyan abubuwan dake cima kwalejin tuwo a kwarya.
Dr. Maigari Abdu yayi kira ga masu hannu da shuni dasu gina gidaje daf da kwalejin domin badawa haya ga dalibai a cikin saukakakken farashi amatsayin gudummuwarsu ga bunkasa ilimi.
Haka kuma ya jaddada bukatar dake akwai ga ‘yan kungiyar tsaffin daliban kwalejin a kodayaushe su rika ziyartar makaranta domin tanatnce na’u’rorin kayayyakin koyo da koyarwar da zasu samar a matsayin tallafi.
Dr. Maigari Abdu yace kwalejin tana da dalibai sama da 8,000 don haka akwai bukatar kara fadada masallacin da take dashi domin masallata su kara samun wuraren gudanar da ibada.
Shugaban Kwalejin ilimi ta Isa Kaita ya koka matuka akan karancin ruwa da ake samu a gidajen haya na dalibai maza inda yayi kira ga mutane a garin Dutsinma dasu taimaka ma daliban.
Dr. Maigari Abdu ya tunatar da al’ummar garin Dutsinma dasu yi koyi da sauran jihohi ta fuskar bunkasa cigaban ilimi kasancewar gwamnati ita kadai ba zata iya warware dukkanin bukatun al’umma ba.
Tun da farko, shugaban kungiyar tuntuba na Dutsinma Bello Isiyaku ya yima shugaban kwalejin dan takaitaccen bayani akan aikace-aikacen kungiyar da kuma bukatar hadin gwiwa domin cigaban yankin.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Gidauniyar Ogan Boye Da Kungiyar Matasan Likitoci Sun Tallafa Wa Marasa Lafiya

Next Post

Sojoji Sun Karyata Labarin Ceto ’Yan Matan Chibok

RelatedPosts

Hadiza Usman

Hadiza Bala Usman Ta Yi Ta’aziya Ga Iyalan Marigayi Dikko Inde

by Sagir Abubakar
1 hour ago
0

Daga Abdullahi Sheme A ranar juma'ar da ta gabatane shugabar...

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

by Sagir Abubakar
1 hour ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Masana da masu ruwa da tsaki...

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

by Sagir Abubakar
2 hours ago
0

Rahotanni daga jihar Zamfara sun tabbatar da cewa an ceto...

Next Post
Hotunan Sabbin Shugabannin Rundunonin Tsaro

Sojoji Sun Karyata Labarin Ceto ’Yan Matan Chibok

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version