• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Fyade
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu wata tsohuwar shugabar makaranta, ‘yar asalin Isra’ila da laifin cin zarafin wasu dalibanta biyu a wata makarantar Yahudawa da ke Australia.

Kotu a birnin Melbourne na Australia ta samu Malka Leifer da laifin cin zarafin wasu yara mata guda biyu Dassi Erlich da Elly Sapper tsakanin shekarun 2003 zuwa 2007.
Sai dai, ba a same ta da laifin yin lalata da yarinya ta uku da aka tuhume ta a kai ba, Nicole Meyer.

  • Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

Leifer, mai shekara 56 ta musanta zarge-zargen da aka yi mata tun da farko, kuma ta kwashe shekaru tana kokarin ganin ba a mayar da ita Australia daga Isra’ila ba.

Sai dai a 2021 ne kotu ta ba da umurnin mayar da ita Australia din daga Isra’ila.
Daliban sun ce Leifer ta yi lalata da su a cikin aji, da kuma lokutan da suka kai ziyara gidanta daga makaranta.

Mai gabatar da kara Justin Lewis ya ce Leifer ta bayyana alamun cewa ita mai son bin mata ce.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Ya ce ta yi amfani da matsayinta da kuma kuruciyar yaran da rashin saninsu game da abubuwan da suka shafi saduwa wajen ganin ta cimma nufinta.

Yaran a wancan lokacin ba su san komai game da lalata ba, saboda irin tarbiyyar da aka ba su, inda aka hore su kan tsarin rayuwa ta tsantsar bin addinin Yahudu. In ji mai gabatar da karar.

Ya kara da cewa “Kasancewar ta san an yi watsi da su a gida, sai ta nuna tamkar tana son su, kuma ta ce musu tana taimakon su ne.”

Sai dai lauyan wadda ake zargi, Ian Hill ya ce zarge-zargen ba su da tushe.
Ayarin masu kare ta din sun ce ba ta samu damar kare kanta yadda ya kamata ba, saboda tsawon lokaci bayan faruwar lamarin.

Leifer ta tsere zuwa Isra’ila bayan da aka tayar da maganar zarge-zargen.
Sai dai an kama ta a 2014 bayan da Australia ta bukaci hakan, amma shekara biyu da ta wuce, sai wata kotun Isra’ila ta soke batun mayar da ita Australia, inda kotun ta ce tana da tabin hankali.

Amma masu bincike na farin kaya sun dauko hotunanta tana sayen kaya a kanti da kuma ajiye kudi a banki, abin da ya sanya Isra’ilar ta sake kama ta tare da gurfanar da ita a kotu cikin watan Fabrairun 2018.

Sannan bayan kwashe mako biyu ana sauraron karar an samu Leifer da laifi 18 wadanda suka jibanci cin zarafin Ms Erlich da Ms Sapper.

Za a yanke wa Leifer hukunci nan gaba kadan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

Next Post

GORON JUMA’A

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

7 days ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

7 days ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.