• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’umma dai sun zura ido su ga yadda zata kaya a shari’ar da aka fara ta wani matashi dan shekara 18 mai suna Aliyu Sanusi Umar, wanda ya yi sanadin yanke kafar wata yarinya daliba ‘yar shekara 16 Fatima Sulaiman a Jihar Sakkwato.

Shari’ar dai ta dauki hankalin jama’a sobada ana ganin kamar ana sako-sako da lamarin, musamman duba da fitowar da aka yi kotu a baya wanda ba a yi zaman shari’ar ba.

  • Magidanci Ya Nemi Matarsa Ta Biya Naira Miliyan 1.6 Kafin Ya Sake Ta A Kaduna
  • Shugaba Xi Ya Ba Da Umarnin Ba Da Fifiko Ga Ceton Rayuka A Gundumar Luding Da Girgizar Kasa Ta Aukawa

Labarin Fatima Sulaiman daliba ‘yar shekara 16 da ta rasa kafarta sanadiyyar bige ta da mota da Aliyu Sanusi Umar ya yi, lokacin da suke murnar kammala jarabawar NECO, ba bakon abu bane ga duk mai amfani da kafafen sada zumunta ko kafafen watsa labarai.

Fatima Sulaiman, ta ce yaron ba dan makarantar su bane kuma daga farko sai da aka kore shi da ya shigo makarantar inda daliban ke wasan murnar kammala jarabawa.

Ta ce bayan an tashi makarantar sun fito waje sai yaran da ke wasan suka dauko motoci suna wasa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

A cewarta su kuma suna zaune su uku suna jiran a zo daukar su sai motar ta nufo wurin da suke zaune, biyu daga cikin daliban da ke zaune suka gudu ita ma ta yunkura ta gudu sai ta fadi motar ta murkushe ta, ta ce tana neman a yi mata adalci ga halin da ta samu kanta ciki.

Bayan da jama’a suka yi ta yada hotonan wata fitowa kotun da aka gurfanar da yaron wadanda suke cike da shakku, yanzu dai kotun ta zauna cikin tsattsauran tsaro, inda aka tuhumi yaron da laifuka uku da suka hada da tukin mota ba tare da lasisi ba, tukin ganganci da kuma yin sanadin samuwar mummunan rauni.

A zaman kotun dai lauya mai kare wanda ake zargi, Jacob Ochidi SAN, ya nemi bukatar bayar da yaron beli domin a cewarsa laifukan da ake tuhumarsa ba manyan laifukan da ba a bayar beli ba ne.

“Doka ta ce ana bayar da beli ga laifukan da ba manyan laifuka sai in akwai wasu kwararan dalilai na kin bayar da shi, to a wannan shara’ar babu dalilan da kan iya hana a bayar da shi beli, muna tausaya wa yarinyar da iyayenta a kan yanayin da suka shiga, dukanmu ‘yan Adam muke abin da ya faru abin tausayi ne don haka muke tausaya wa iyayenta”

Sai dai lauyan masu shigar da kara, Jamilu Malami, ya kalubalanci wannan bukatar.

Ya ce, “lauyoyin yaron sun shigar da bukatar beli amma dai bangaren gwamnati da bangaren yarinyar sun ki aminta, domin sun samu wani bayanin sirri cewa yaron ya samu gurbin karatu a kasar waje don haka akwai yiwuwar zai iya barin kasar nan kowane lokaci, sannan kuma akwai yiwuwar cewa ko don lafiyar shi ya kamata a bar shi gidan gyaran hali har kura ta kwanta.”

Alkalin kotun majistire, Mariya Haruna Dogon Daji, ta dage zaman zuwa 8 ga wannan wata don yanke hukunci a kan bayar da belin ko akasin haka.

Mutane da dama na ganin dacewar hukunta yaron don zama izina ga na baya masu irin wannam dabi’a tasa ta wasa da mota.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BeliHukunciKotuMatashiMatashiyaRasa KafaSakkwatoShari'aTuhuma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Magidanci Ya Nemi Matarsa Ta Biya Naira Miliyan 1.6 Kafin Ya Sake Ta A Kaduna

Next Post

Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

Related

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

16 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

23 hours ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

23 hours ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

1 day ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

1 day ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

2 days ago
Next Post
Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.