ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tafka Gumurzu, Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram Da Yawa, Wasu Sun Miƙa Wuya

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Sojoji

Rundunar haɗin gwuiwa ta MNJTF ta yi nasarar kai wani sumame da ya yi sanadin miƙa wuyar ƴan ta’addar ƙungiyar IS guda uku tare da kuɓutar da mutane 34 da suka yi garkuwa da su, da suka haɗa da mata da ƙananan yara daga yankin kudancin tafkin Chadi.

Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi, babban jami’in yaɗa labarai na rundunar soji na MNJTF, ya bayyana cewa, a ranar 15 ga watan Yuni, 2024, aikin kakkaɓe ƴan ta’addan a ƙauyukan Mazuri, Itsari, Mudu, da Maleri ya kai ga tarwatsa sansanonin ‘yan ta’adda tare da kashe wani dan tada kayar baya.

  • NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2
  • Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi

A ranar 17 ga Yuni, 2024, mayakan ISWAP uku daga sansanin Jabilaram da ke tafkin Chadi, waɗanda aka bayyana sunayensu da Babakura Abubakar, Abacha Kyari, da Mohammad Adam, sun miƙa wuya ga dakarun sa-kai. Yanzu haka dai ana ci gaba da yi wa mayakan tambayoyi domin samun ƙarin bayanan sirri kan ayyukan ta’addanci.

ADVERTISEMENT
Mayaƙan ISWAP da suka miƙa wuya
Wasu daga cikin waɗanda Sojoji suka ceto

Wannan ci gaban wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na raunana karfin aiki da kwarin gwiwar duk ƴan ta’adda a yankin.

A ci gaba da inganta nasarar hare-haren da aka kai a ranar 9 ga Yuni, 2024, a Kollaram, sun lalata na’urori masu fashewa da suka haɗa da ƙunar bakin wake guda uku da ke shirin kai wani gagarumin hari.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Mayaƙan ISWAP da suka miƙa wuya
Mayaƙan ISWAP da suka miƙa wuya

Manjo Janar Ibrahim Sallau Ali, Kwamandan Rundunar MNJTF, ya yaba da bajintat sojojin tare da jaddada aniyar rundunar na kawar da ta’addanci, tabbatar da tsaron fararen hula, da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tafkin Chadi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Afrika ta Kudu

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Afrika ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.