ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi

by Sani Anwar
2 years ago
Tsaro

Kungiyar Matasan Nijeriya Kan Harkokin Tsaro (CONYSSA), ta shirya taron masu ruwa da tsaki na ƙasa; domin tattaunawa a kan shawawarin da ake yi game da samar da ‘yansandan jiha a faɗin jihohi 36 na tarayya wanda aka gudanar a Cibiyar Bunƙasa Al’amuran Sojoji da ke Abuja (Army Resource Centre).

Da yake yin nasa wajibin a wajen taron da aka shirya tare da haɗin gwiwar Rundunar ‘Yansandan Nijeriya, Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Dakta Isa Yuguda ya yi tsokaci kan cewa, wajibi ne a zurfafa bincike a kan ƙalubalen da ke fuskantar jami’an ‘yansanda da sauran jami’an tsaron wannan ƙasa, matuƙar ana so su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu.

Yuguda ya ƙara da cewa, a matsayin Nijeriya ta ƙasa; dole ne ta ƙara ƙaimi wajen sanin matsalolin da ke addabar waɗannan jami’ai, kafin ta kai ga cimma nasarar da take buƙata a tsakaninsu.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara jaddada cewa, “ƙasar da take da ingantaccen tsaro, ita ce wadda zuba jari ke matuƙar bunƙasa a cikinta. Don haka, kafin Nijeriya ta kai ga matsayin da ake buƙata a fannin tsaro, dole ne ta sake jajircewa tare da samun mutane masu matuƙar kishi, ɗa’a, ƙwarewa, aikin yi da kuma adalci a tsakanin al’umma.

Tsaro
Har ila yau, tsohon gwamnan; ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga sauran al’ummar ƙasa, domin su farka tare da kasancewa cikin shiri; don sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na tallafa wa gwamnati tsakaninsu da Allah, domin ganin an samu ci gaban ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Kazalika, ya buƙaci mahalarta wannan taro da a koda-yaushe su riƙa tunanin samar da mafita tare da ci gaban ƙasar baki-ɗaya.
Ya ci gaba da cewa, “Muna buƙatar gyara ‘yansandanmu, domin abin tambaya shi ne; shin sun samu horo mai kyau, suna samun albashi mai kyau, suna da ingantattatun kayan aiki, suna samun horon da ya kamata ɗansanda ya samu ko kuma a’a kawai abin da ake cewa; muna ɗansanda ne?
Saboda haka, “Wajibi ne mu fara magance matsalolin da suka shafi ‘yansanda, maimakon ƙirƙirar wasu ‘yansandan waɗanda za su iya zama haɗari ko barazana da makamai a hannunsu.”

Haka zalika, shi ma a nasa tsokacin; Mai Martaba Cif Ayini Clement, wanda yake da ra’ayin samar da waɗannan ‘yansanda na jihohi ya bayyana cewa, akwai buƙatar a ƙara wa ‘yansandan tarayya ƙwarin gwiwa, domin samun damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Tsaro
Cif ya ƙara da cewa, fa’idar samar da ‘yansandan jihohi ita ce, duk yankin da aka ɗauki ɗansanda aiki; ya san lungu da saƙo na wannan waje tare da dukkanin al’ummar da ke zaune a yankin.

Haka zalika, shi ma Darakta Janar mai kula da harkokin tsaro da binciken shari’a a Nijeriya, Dakta Okocha Morgan; ya yi kira ga gwamnati da ta taka muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi tare da sake fasalin harkokin tsaro a Nijeriya, wanda ya haɗa da horar da ma’aikata da kuma ɗaukar wasu ƙwararrun ma’aikatan.

Bugu da ƙari, tun da farko; Darakta Janar na wannan ƙungiya ta Haɗin Kan Matasan Nijeriya Kan Harkokin Tsaro (CONYSA), Ambasada Ade Emmanuel ya ce, manufar wannan taro shi ne; tattaunawa a kan muhimmanci ko rashin muhimmancin samar da ‘yansandan jihohi da ake ta faman taƙaddama a kansa.

“Babu shakka, matasa na da gudunmawar da za su iya bayarwa; domin yaƙi da rashin tsaro matuƙar an yi amfani da su yadda ya dace, sannan ‘yansandan jihohi na iya samun ci gaba a wasu ƙasashen da suka ci gaba; suke da kuma kishin ƙasa fiye da mu, amma aiwatar da shi a nan ko shakka babu; na iya haifar da mummunan rikici.

Saboda haka, “ya kamata gwamnatocin jihohi su yi aiki yadda ya kamata da ‘yansandan tarayya, domin samun sauƙi, inganci da kuma ɗorewar zaman lafiya a faɗin wannan ƙasa baki-ɗaya.

Har ila yau, taron ya samu halartar wakilan hukumomin soja da na jami’an tsaro daban-daban a Nijeriya da kuma sauran masu ruwa da tsaki.

Tsaro
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.