• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wawashe Shaguna Yayin Da Ake Ci Gaba Da Zanga-zanga A Burtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Kasashen Ketare
0
An Wawashe Shaguna Yayin Da Ake Ci Gaba Da Zanga-zanga A Burtaniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firayim Ministan Burtaniya Keir Starmer ya yi gargadi mai tsanani ga masu zanga-zangar ‘yan ra’ayin rikau, yana mai alkawarin wadanda ke da hannun a tarzomar Ingila mafi muni cikin shekaru 13 za su yi nadamar abin da suka aikata.

Zanga-zangar da aka fara ta auku ce bisa kisan wasu yara uku wacce ta bazu a fadin kasar.

  • Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase
  • Yadda Aka Kashe Manoma 8 Da Sace Dabbobi 1,260 A Sakkwato

A Rotherham, Kudancin Yorkshire, masu zanga-zangar adawa da shigar bakin haure sun farfasa tagogi a wani otal da masu neman mafaka suke ciki.

LEADERSHIP Hausa ta rawaito cewa rikicin, wanda ya samo asali ne sakamakon rashin fahimtar da aka samu game da wani hari da aka yi a Southport, ya shafi garuruwa da birane da dama, wanda ya kai ga arangama tsakanin masu zanga-zangar da ‘yansanda.

Da yake jawabi ga al’ummar kasar ta gidan talabijin, Starmer ya ce, “Na ba da tabbacin za ku yi nadamar shiga cikin wannan matsalar. Ko kai tsaye ko wadanda ke yin wallafa bayanai ta intanet, sannan su gudu.” Ya yi Allah wadai da ‘yan daba kuma ya sha alwashin gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

Hotunan da aka watsa a BBC sun nuna yadda masu tarzomar suka tilasta shiga cikin Holiday Inn Edpress da ke Rotherham tare da tura wani abu da ke cin wuta a ginin. Har yanzu babu tabbas ko masu neman mafaka suna ciki a lokacin.

A Middlesbrough, daruruwan masu zanga-zangar sun fuskanci ‘yansandan kwantar da tarzoma, inda suka rika jifan jami’an, da duwatsu, gwangwani, da tukwane. An kama mutum sama da 90 bayan wata arangama da aka yi a wajen gangamin hannun dama a Liberpool, Manchester, Bristol, Blackpool, Hull, da Belfast.

Masu tarzoma sun yi ta jifan ‘yansanda duwatsu da kwalabe, inda suka jikkata jami’an da dama, kuma suka yi awon gaba da kayan shaguna da kona su, tare da yin kururuwa na kyamar Musulunci a lokacin da suke artabu da masu zanga-zangar. Rikicin dai shi ne mafi muni tun bayan tarzomar 2011 da ta biyo bayan kisan da ‘yansanda suka yi wa wani dan kabilar baki a Arewacin Landan.

Tiffany Lynch na hukumar ‘yansanda ta Ingila da Wales ya ce, “Yanzu muna ganin yadda matsala ta mamaye manyan birane da garuruwa.”

An fara tarzomar ce a Southport a daren ranar Talata bayan harin wuka da aka kai a ranar litinin a wani gidan rawa mai taken Taylor Swift. Wanda ake zargin, Adel Rudakubana mai shekaru 17, ana zarginsa da kashe yara uku tare da raunata wasu goma. Jita-jitar karya game da tarihinsa a shafukan sada zumunta ce ta haifar da tarzoma.

‘Yansanda sun danganta tashin hankalin da magoya bayan kungiyar kare hakkin bil’adama ta Ingila wato English Defence League da ke da alaka da kyamar kwallon kafa.

Masu tayar da kayar baya sun kai hari a akalla Masallatai biyu, lamarin da ya sa ma’aikatar harkokin cikin gidan Burtaniya ta ba da sabbin matakan tsaro na gaggawa ga wuraren ibada na Musulunci.

An dai shirya gangami a karkashin taken “Ya isa” a kafifin sada zumunta na dama. Mahalarta taron sun daga tutocin Ingilishi da na Biritaniya tare da rera taken “Dakatar da jiragen ruwa,” da ke nuni da bakin haure da ke tafiya Birtaniyya daga Faransa ba bisa ka’ida ba.

Masu zanga-zangar adawa da mulkin Fascist sun gudanar da zanga-zangar adawa da shi a garuruwa da dama. A Leeds, sun yi ta rera wakar “Nazi sun kashe kan titunan mu” yayin da masu zanga-zangar dama suka amsa da “Ba Ingilishi ba ne kuma.”

Rahotanni sun nuna cewa ba dukkan tarukan ne suka koma tashin hankali ba. Wata zanga-zangar lumana a Aldershot an ga mahalarta rike da allunan da ke rubuta “Dakatar da mama.”

Gwamnatin Starmer dai na fuskantar jarrabawa tun farko wajen tunkarar tarzomar, bayan da aka zabe ta wata guda da ya gabata bayan da jam’iyyar Labour ta samu gagarumin rinjaye kan jam’iyyar Conserbatibes.

Kotu Ta Daure Masu Zanga-zangar Kyamat Baki A Burtaniya

A halin da ake ciki kuma, wata kotu a Birtaniya ta yanke hukuncin dauri kan wasu mutane da aka samu da laifin tayar da tarzoma tun zanga-zangar da ta barke sama da mako daya.

An yanke wa mutanen uku hukuncin shekara uku a gidan yari saboda shiga zanga-zangar a Liberpool.

Wannan ne matakin yanke hukunci cikin hanzari wanda gwamnati take son ya zama darasi, ya kuma dakile yiwuwar tashin hankali a gaba.

Rikicin na kin jinin ‘yan ci-rani ko baki shi ne mafi muni da ya bazu zuwa sassan Ingila da Arewacin Ireland.

An kama kimanin mutum 400 a garuruwa da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BurtaniyaWawasoZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Tsinke Sarkar Rashin Adalci A Nijeriya Nakuda 

Next Post

Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga ‘Yan Bautar Ƙasa Ba – NYSC

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

19 hours ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

2 days ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

7 days ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga ‘Yan Bautar Ƙasa Ba – NYSC

Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga 'Yan Bautar Ƙasa Ba - NYSC

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.