• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wawashe Shaguna Yayin Da Ake Ci Gaba Da Zanga-zanga A Burtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kasashen Ketare
0
An Wawashe Shaguna Yayin Da Ake Ci Gaba Da Zanga-zanga A Burtaniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firayim Ministan Burtaniya Keir Starmer ya yi gargadi mai tsanani ga masu zanga-zangar ‘yan ra’ayin rikau, yana mai alkawarin wadanda ke da hannun a tarzomar Ingila mafi muni cikin shekaru 13 za su yi nadamar abin da suka aikata.

Zanga-zangar da aka fara ta auku ce bisa kisan wasu yara uku wacce ta bazu a fadin kasar.

  • Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase
  • Yadda Aka Kashe Manoma 8 Da Sace Dabbobi 1,260 A Sakkwato

A Rotherham, Kudancin Yorkshire, masu zanga-zangar adawa da shigar bakin haure sun farfasa tagogi a wani otal da masu neman mafaka suke ciki.

LEADERSHIP Hausa ta rawaito cewa rikicin, wanda ya samo asali ne sakamakon rashin fahimtar da aka samu game da wani hari da aka yi a Southport, ya shafi garuruwa da birane da dama, wanda ya kai ga arangama tsakanin masu zanga-zangar da ‘yansanda.

Da yake jawabi ga al’ummar kasar ta gidan talabijin, Starmer ya ce, “Na ba da tabbacin za ku yi nadamar shiga cikin wannan matsalar. Ko kai tsaye ko wadanda ke yin wallafa bayanai ta intanet, sannan su gudu.” Ya yi Allah wadai da ‘yan daba kuma ya sha alwashin gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya.

Labarai Masu Nasaba

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

Hotunan da aka watsa a BBC sun nuna yadda masu tarzomar suka tilasta shiga cikin Holiday Inn Edpress da ke Rotherham tare da tura wani abu da ke cin wuta a ginin. Har yanzu babu tabbas ko masu neman mafaka suna ciki a lokacin.

A Middlesbrough, daruruwan masu zanga-zangar sun fuskanci ‘yansandan kwantar da tarzoma, inda suka rika jifan jami’an, da duwatsu, gwangwani, da tukwane. An kama mutum sama da 90 bayan wata arangama da aka yi a wajen gangamin hannun dama a Liberpool, Manchester, Bristol, Blackpool, Hull, da Belfast.

Masu tarzoma sun yi ta jifan ‘yansanda duwatsu da kwalabe, inda suka jikkata jami’an da dama, kuma suka yi awon gaba da kayan shaguna da kona su, tare da yin kururuwa na kyamar Musulunci a lokacin da suke artabu da masu zanga-zangar. Rikicin dai shi ne mafi muni tun bayan tarzomar 2011 da ta biyo bayan kisan da ‘yansanda suka yi wa wani dan kabilar baki a Arewacin Landan.

Tiffany Lynch na hukumar ‘yansanda ta Ingila da Wales ya ce, “Yanzu muna ganin yadda matsala ta mamaye manyan birane da garuruwa.”

An fara tarzomar ce a Southport a daren ranar Talata bayan harin wuka da aka kai a ranar litinin a wani gidan rawa mai taken Taylor Swift. Wanda ake zargin, Adel Rudakubana mai shekaru 17, ana zarginsa da kashe yara uku tare da raunata wasu goma. Jita-jitar karya game da tarihinsa a shafukan sada zumunta ce ta haifar da tarzoma.

‘Yansanda sun danganta tashin hankalin da magoya bayan kungiyar kare hakkin bil’adama ta Ingila wato English Defence League da ke da alaka da kyamar kwallon kafa.

Masu tayar da kayar baya sun kai hari a akalla Masallatai biyu, lamarin da ya sa ma’aikatar harkokin cikin gidan Burtaniya ta ba da sabbin matakan tsaro na gaggawa ga wuraren ibada na Musulunci.

An dai shirya gangami a karkashin taken “Ya isa” a kafifin sada zumunta na dama. Mahalarta taron sun daga tutocin Ingilishi da na Biritaniya tare da rera taken “Dakatar da jiragen ruwa,” da ke nuni da bakin haure da ke tafiya Birtaniyya daga Faransa ba bisa ka’ida ba.

Masu zanga-zangar adawa da mulkin Fascist sun gudanar da zanga-zangar adawa da shi a garuruwa da dama. A Leeds, sun yi ta rera wakar “Nazi sun kashe kan titunan mu” yayin da masu zanga-zangar dama suka amsa da “Ba Ingilishi ba ne kuma.”

Rahotanni sun nuna cewa ba dukkan tarukan ne suka koma tashin hankali ba. Wata zanga-zangar lumana a Aldershot an ga mahalarta rike da allunan da ke rubuta “Dakatar da mama.”

Gwamnatin Starmer dai na fuskantar jarrabawa tun farko wajen tunkarar tarzomar, bayan da aka zabe ta wata guda da ya gabata bayan da jam’iyyar Labour ta samu gagarumin rinjaye kan jam’iyyar Conserbatibes.

Kotu Ta Daure Masu Zanga-zangar Kyamat Baki A Burtaniya

A halin da ake ciki kuma, wata kotu a Birtaniya ta yanke hukuncin dauri kan wasu mutane da aka samu da laifin tayar da tarzoma tun zanga-zangar da ta barke sama da mako daya.

An yanke wa mutanen uku hukuncin shekara uku a gidan yari saboda shiga zanga-zangar a Liberpool.

Wannan ne matakin yanke hukunci cikin hanzari wanda gwamnati take son ya zama darasi, ya kuma dakile yiwuwar tashin hankali a gaba.

Rikicin na kin jinin ‘yan ci-rani ko baki shi ne mafi muni da ya bazu zuwa sassan Ingila da Arewacin Ireland.

An kama kimanin mutum 400 a garuruwa da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BurtaniyaWawasoZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Tsinke Sarkar Rashin Adalci A Nijeriya Nakuda 

Next Post

Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga ‘Yan Bautar Ƙasa Ba – NYSC

Related

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

60 minutes ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

1 day ago
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka
Kasashen Ketare

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

1 day ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

2 days ago
Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
Kasashen Ketare

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

1 week ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

2 weeks ago
Next Post
Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga ‘Yan Bautar Ƙasa Ba – NYSC

Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga 'Yan Bautar Ƙasa Ba - NYSC

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

July 14, 2025
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.