• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yanke Wa Da Nijeriya Hukuncin Daurin Shekara 4 Saboda Damfara A Amurka

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
An Yanke Wa Da Nijeriya Hukuncin Daurin Shekara 4 Saboda Damfara A Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotu a Kasar Amurka ta yanke wa wani dan Nijeriya mai suna Solomon Ekunke Okpe, dan shekaru 31, hukuncin daurin shekaru hudu da wata daya a gidan yari, bisa samunsa da hannu a wata kungiyar masu aikata laifuka ta Intanet.

Kungiyar ta masu aikata laifuka da ke aiki a kasashen Najeriya da Malesiya, da dai sauran wurare, wadanda suka aiwatar da zamba ta hanyar amfani da yanar gizo.

  • Atiku Ba Zai Yi Ritaya Daga Siyasa Ba -Dino Melaye
  • Kasashen Sin Da Honduras Sun Kulla Huldar Diflomasiyya

A cewar takardun kotu, tsakanin watan Disamba na 2011 zuwa Janairun 2017, Solomon Ekunke Okpe tare da abokansa da suka aikata laifin, sun kirkiri wata hanyar damfara ta amfani da hanyar imel na kasuwanci (BEC), na aiki-daga gida, da fidda kudi ta amfin da check din banki, soyayya, katin banki don damfarar mutane da ba su ji ba basu gani ba, bankuna, da masana’antu a Amurka da sauran wurare, wanda yin hakan zai haddasa asarar fiye da dala miliyan daya ga Amurkawa da wadanda lamarin ya shafa. Cikin wadanda lamarin ya rutsa da su har da kamfanin First American Holding, da bankin MidFirst.

Okpe da abokansa sun kaddamar da hare-haren satar bayanan sirri na imel don satar muhimman bayanan mutane, da yin kutse ta yanar gizo, don aiwatar da damfarar, suka rika yin amfani da bayanan suna damfarar mutane, bankuna, masana’antu, sun kuma yi safarrar, da amfani da katunan banki da aka sace don ci gaban damfararsu.

Okpe da hadakarsa sun kuma gudanar da zamba ta hanyar soyayya ta shafukan soyayya na yanar gizo, da nuna sha’awar mu’amalar soyayya da mutane da sunayen karya, don mutane su tura musu kudade zuwa ketare ko zamba ta hanyar waya. Okpe ya sa dubban mutanen sun fuskanci asarar dubban daloli ta hanyar soyayya.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

A baya dai an kama Okpe a Malaysia bisa bukatar Amurka kuma an tsare shi sama da shekaru biyu a lokacin bayan da ya nemi a mika shi ga Amurka.

A ranar 20 ga Maris, aka yanke wa daya daga cikin wadanda suka hada baki da Okpe, Johnson Uke Obogo, hukuncin daurin shekara daya da kwana daya a gidan yari, dangane da rawar da ya taka wajen zambar kudade.

FBI ta gano adadin wadanda abin ya shafa, duk da haka, akwai wadanda har yanzu ba a tantance su ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaDamfaraDan NijeriyaIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kwaso ‘Yan Nijeriya 151 Da Suka Makale A Libya

Next Post

Ahmed Musa Ya Kamo Tarihin Da Zidane Ya Kafa A Kwallon Kafa

Related

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

2 hours ago
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Labarai

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

3 hours ago
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi
Labarai

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

4 hours ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Manyan Labarai

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

5 hours ago
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 
Manyan Labarai

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

6 hours ago
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato
Tsaro

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

18 hours ago
Next Post
Ahmed Musa Ya Kamo Tarihin Da Zidane Ya Kafa A Kwallon Kafa

Ahmed Musa Ya Kamo Tarihin Da Zidane Ya Kafa A Kwallon Kafa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.