• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yanke Wa Da Nijeriya Hukuncin Daurin Shekara 4 Saboda Damfara A Amurka

by Sadiq
3 years ago
Nijeriya

Wata kotu a Kasar Amurka ta yanke wa wani dan Nijeriya mai suna Solomon Ekunke Okpe, dan shekaru 31, hukuncin daurin shekaru hudu da wata daya a gidan yari, bisa samunsa da hannu a wata kungiyar masu aikata laifuka ta Intanet.

Kungiyar ta masu aikata laifuka da ke aiki a kasashen Najeriya da Malesiya, da dai sauran wurare, wadanda suka aiwatar da zamba ta hanyar amfani da yanar gizo.

  • Atiku Ba Zai Yi Ritaya Daga Siyasa Ba -Dino Melaye
  • Kasashen Sin Da Honduras Sun Kulla Huldar Diflomasiyya

A cewar takardun kotu, tsakanin watan Disamba na 2011 zuwa Janairun 2017, Solomon Ekunke Okpe tare da abokansa da suka aikata laifin, sun kirkiri wata hanyar damfara ta amfani da hanyar imel na kasuwanci (BEC), na aiki-daga gida, da fidda kudi ta amfin da check din banki, soyayya, katin banki don damfarar mutane da ba su ji ba basu gani ba, bankuna, da masana’antu a Amurka da sauran wurare, wanda yin hakan zai haddasa asarar fiye da dala miliyan daya ga Amurkawa da wadanda lamarin ya shafa. Cikin wadanda lamarin ya rutsa da su har da kamfanin First American Holding, da bankin MidFirst.

Okpe da abokansa sun kaddamar da hare-haren satar bayanan sirri na imel don satar muhimman bayanan mutane, da yin kutse ta yanar gizo, don aiwatar da damfarar, suka rika yin amfani da bayanan suna damfarar mutane, bankuna, masana’antu, sun kuma yi safarrar, da amfani da katunan banki da aka sace don ci gaban damfararsu.

Okpe da hadakarsa sun kuma gudanar da zamba ta hanyar soyayya ta shafukan soyayya na yanar gizo, da nuna sha’awar mu’amalar soyayya da mutane da sunayen karya, don mutane su tura musu kudade zuwa ketare ko zamba ta hanyar waya. Okpe ya sa dubban mutanen sun fuskanci asarar dubban daloli ta hanyar soyayya.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

A baya dai an kama Okpe a Malaysia bisa bukatar Amurka kuma an tsare shi sama da shekaru biyu a lokacin bayan da ya nemi a mika shi ga Amurka.

A ranar 20 ga Maris, aka yanke wa daya daga cikin wadanda suka hada baki da Okpe, Johnson Uke Obogo, hukuncin daurin shekara daya da kwana daya a gidan yari, dangane da rawar da ya taka wajen zambar kudade.

FBI ta gano adadin wadanda abin ya shafa, duk da haka, akwai wadanda har yanzu ba a tantance su ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Next Post
Ahmed Musa Ya Kamo Tarihin Da Zidane Ya Kafa A Kwallon Kafa

Ahmed Musa Ya Kamo Tarihin Da Zidane Ya Kafa A Kwallon Kafa

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.