Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Yi Garkuwa Da Dan Majalisa A Taraba

by Muhammad
December 9, 2020
in LABARAI
1 min read
An Yi Garkuwa Da Dan Majalisa A Taraba
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muh’d Shafi’u Saleh,

Wasu da’ake zargin masu garkuwa da mutanene, sunyi garkuwa da dan majalisar dokokin jihar Taraba Honarabul Bashir Muhammad Nape, dake wakiltar mazabar Nguroji, a gidansa dake Jalingo fadar jihar.

samndaads

Rahotannin dake fitowa daga inda lamarin ya auku sun tabbatar da cewa ‘yan bindigar da su ka saceshin sun taho da yawa, inda su ka rika harbe-harbe sun kori ‘yan bangar dake gadi a gidan dan majalisar.

“Yan bindigar sun taho da yawa, sun farma ‘yan banga da ke gadin gidan su ka kutsa cikin gidan kai tsaye zuwa har inda dan majalisar ke kwana..

“An ce ‘yan bindigar sun zo gidan ne da babura da misalin karfe 1:00 na daren yau Laraba, yayin da mutane ke barci.

“Da shigarsu gidan, su ka kwace duk wayoyin salularshi da na mutanen da ke gidan.

“Daganan ne su ka tafi da mamban sun hau babur dinsu sukl ka tisa keyarsa ba tare da sunce komai ba,” in ji wani da ke kusa da gidan dan majalisar.

Wannan dai shi ne karo na biyu da ‘yan bindiga ke sace dan majalisar dokokin jihar Taraba cikin shekarun guda.  Haka kuma a 30 ga Disamban 2017, an sace dan majalisar dokokin jihar mai wakiltar Takum 1, a garin Takum lokacin da ya je domin gudanar da bukukuwan karshen shekara, inda su ka kasheshi bayan an biya kudin fansa.

Kokarin jin tabakin rundunar ‘yan sandan jihar Taraba kan wannan batun ya ci tura, domin kuwa Kakakin rundunar DSP David Misal, baya tafiya lokacin hada rahoton.

SendShareTweetShare
Previous Post

APC Ta Dauki Tsauraran Matakan Gyara

Next Post

CCG Ya Shirya Taron Tattaunawa Da Jakadu Da Wakilan Ofisoshin Jakadancin Kasashe Dake Sin Kan Shirin Raya Kasa Da Yarjejeniyar AfPTA

RelatedPosts

'Ya’ya Mata

Hukumar Ilimin Bai Daya ‘UBEC’ Ta Gina Makarantar ‘Ya’ya Mata Zalla A Katsina

by Sulaiman Ibrahim
13 mins ago
0

Hukumar ilimi bai daya ta kasa ta gina wata makaranta...

Zaben Kananan Hukumomin Kano

Zaben Kananan Hukumomin Kano: Mun Gamsu Da Yadda Ya Gudana A Tofa – Idris Unguwa

by Sulaiman Ibrahim
18 mins ago
0

Kwamishinan ma'aikatar ayyuka na jahar Kano.Alhaji Idris Garba Unguwar Rimi...

Sheik Karibullah

Sheik Karibullah Ya Nada Alhaji Kabiru Sani Kwangila Khadimul Nabiyya A Taron Maulidin Gidansa

by Sulaiman Ibrahim
56 mins ago
0

A ranar Lahadi ne aka gudanar da Maulidin Manzon Allah...

Next Post
CCG Ya Shirya Taron Tattaunawa Da Jakadu Da Wakilan Ofisoshin Jakadancin Kasashe Dake Sin Kan Shirin Raya Kasa Da Yarjejeniyar AfPTA

CCG Ya Shirya Taron Tattaunawa Da Jakadu Da Wakilan Ofisoshin Jakadancin Kasashe Dake Sin Kan Shirin Raya Kasa Da Yarjejeniyar AfPTA

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version