Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

An Yi Kira Ga ‘Yan Kasuwa Da Su Yi Sassauci Saboda Gabatowar Azumi

by Muhammad
April 2, 2021
in LABARAI
2 min read
Kasuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Muhammad,

An yi kira ga yan kasuwa su rika sassautawa da yin hakuri da da karamar riba musamman a wannan lokaci da Azumin watan ramada ke karatowa.

Wani Matashin dan kasuwa a kasuwar Kantin Kwari Alhaji Sagir Haruna Daurawa ya yi kiran da yake zantawa da ‘yan jarida.

Ya ce, abin takaici ga wasu yan Kasuwar sai irin wannan wata mai albarka yazo wasu ke kokarin tsawwala kayan su yi tsada wanda hakan bai kamata ba.

Alhaji Sagir Haruna wanda shi ne shugaban Shagon “Haruna Daurawa Tedtile” yayi rokon  dan Allah da Annabi kowane kaya na sayarwa ‘yan uwansa ‘yan kasuwa su sayar dashi a matsayinsa  cikin  adalci da kowa zai samu ya fita kunyar iyalinsa.

Sannan ya yi kira ga mata batagari da suke shigowa kasuwa da shiga ta kamala amma su rika sata bai kamata mata da ke da daraja da mutumci ace su ake samu da irin wannan ba don haka, masu irin wannan hali su yi hakuri su daina kar a kamasu ayi musu wulakancinda ta yiwu wani da ya sansu yaje ya fada hakan ya jawo zubewar mutuncinsu dana ya’yansu.

Ya ce kowace mace ta yi hakuri na tsayawa a matsayin da Allah ya ajiyeta domin  zafin nema ba shi ne ke tara wani abu ba ayi hakuri a nemi taimakon Allah sai a sami abinda ake so na halak.

Da ya juya kan yanda ake samun matsalar sadarwa a kasuwar Kwari, ya ce, hakan na jawo musu tangarda da abokan huldarsu harma da iyalansu da basa samun ganawa da su ta waya in bukatar hakan ta taso. Sannan sukan rasa mu’amala da  abokan huldarsu saboda sukan kirasu su kasa samunsu.

Ya ce sai dai yanzu an dan soma ganin saukin matsalar ta sadarwa, saboda mutane sun cire na’ura da suke sawa dake zuko damar kira.

Ya ce,  yakamata kamfanonin waya suzo su duba su baiwa kasuwannin Kano network mai inganci dan kyautata huldarsu da suke a kasuwar da baya wuce na  daga safe zuwa yamma aannan  itama Gwamnati yakamata tasa baki wajen sanya kamfanonin sadarwa kyautata ingancin sadarwa a Kano.

Alhaji Sagir Daurawa ya ce suna hulda da yan kasashen waje daban-daban amma  sakamakon barazanar tsaro huldar ta danyi rauni saboda basa iya zuwa  mutum.bazai iya debo dukiyarsa yazo ko ya turo da ita ba, matsala ta auku ba wanda zai kama dan haka basa son zuwa.

Alhaji Sagir Haruna Daurawa yace koma da an turo da kudi ance ka tura kaya in an tura kayan suma direbobi da suke kaiwa na fadawa cikin barazanar rashin tsaro da sauran matsaloli wannan babaan kalubalene da ake fuskanta da suke rokon Allah ya kawo karshen abin ta baiwa kasarnan zaman lafiya da kwanciyar hankali.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyar RTEAN Ta Bukaci Mambobinta Su Mutunta Dokokin Kasa

Next Post

An Kama Kayan Abinci Da Ake Zargin Gurbatattu Ne A Kano

RelatedPosts

INEC Ta Fara Horas Da Shugabannin Harkar Zaɓe Kan ƙara Yawan Rumfuna

INEC Ta Fara Horas Da Shugabannin Harkar Zaɓe Kan ƙara Yawan Rumfuna

by Sulaiman Ibrahim
15 mins ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kan ta...

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Isra'ila ta ce ta kai harin bama-bamai...

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Wani babban kwamandan ISWAP, Bukar Gana (wanda...

Next Post
Kashe

An Kama Kayan Abinci Da Ake Zargin Gurbatattu Ne A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version