• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masarautar ’Yandoton Daji da ke jihar Zamfara, ta nada kasurgumin dan bindigar nan da ake nema ruwa a jallo, Ado Aleiro, sarautar Sarkin Fulanin ’Yandoto a ranar Asabar.

Aleiro dan bindiga ne da ya yi kaurin suna a ciki da wajen jihar Zamfara.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna
  • Zaben Osun: ‘Yan Nijeriya Na Kallon Mu – Mahmoud Ga Ma’aikatan INEC

A baya gwamnatin Zamfara da wasu jihohi da ke makwabtaka da jihar sun yi kokarin yin sulhu da neman zaman lafiya daga hare-haren da shi da yaransa ke kai wa kauyukan jihar.

An gudanar da bikin nadin ne ’yan sa’o’i bayan masarautar ta sanar da fasa nadin tun da farko.

Sarkin na ’Yandoto, Alhaji Aliyu Marafa tun da farko ya yi shirn nada Aleiron sarautar a ranar Asabar, amma ya dage bikin ’yan sa’o’i sakamakon umarnin gwamnatin jihar, kamar yadda Aminiya ta ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nadin na zuwa ne biyo bayan rawar da masarautar ta taka a baya tsakanin masarautar da ‘yan bindigar da suka addabi karamar hukumar tsafe a jihar.

Gwamnatin jihar dai tun da farko ta ba da umarnin dakatar da nadin ne saboda gudun cece-kucen da hakan zai iya jawowa idan labarin ya fita.

Bikin nadin sarautar dai, wanda aka yi a fadar masarautar ’Yandoton Daji, ya samu halartar Shugaban Karamar Hukumar Tsafe da kuma Kwamishinan Tsaro da Al’amuran Cikin Gida na Jihar, DIG Mamman Tsafe (mai ritaya).

Wata majiya ta shaida cewar “Bikin ya kuma samu halartar shugabannin ’yan bindiga da dama tare da dakarunsu da suka je a kan babura.

“Sun bi ta hanyar Gusau zuwa Funtuwa, inda suka yada zango a Gidan Dawa, inda mutanen garin suka ba su katan-katan na lemukan sha a matsayin gudunmawa,” inji majiyar da ta bukaci a sakaya sunanta.

“Amma babu tabbaci ko shi Aleiron ya yi jawabi yayain nadin, amma daya daga cikin na hannun damansa wanda ya yi jawabi ya koka da yadda ya ce mutane na kiransu da ’yan ta’adda,” inji mazaunin yankin da ya bayyana sunansa da Sufyan.

“Mu ba ’yan fashi ba ne kuma ba ’yan ta’adda ba, amma muddin ana so zaman lafiya ya dawo, dole gwamnatin jiha da ta tarayya su samar mana mu makiyaya da filayen kiwo da makarantu da asibitoci.,”

A baya Aleiro ya yi alkawarin ajiye makamansa, amma daga bisani ya sake kai wasu munanan hare-hare Kananan Hukumomin Tsafe da Faskari da Kankara da ke jihohin Zamfara da Katsina.

Jim kadan da yin haka ne rundunar ’yan sandan Katsina ta sanya la’adar Naira miliyan biyar ga duk wanda ya kawo mata shi.

Tun daga lokacin ne ya yi ta kitsa hare-hare a yankunan Kananan Hukumomin da ke Tsafe da kuma Faskari a jihohin biyu.

Ko a baya gwamnatin Katsina ta sha shirya zaman sulhu tsakaninta da ‘yan bindiga amma alkawarin ba ya dorewa.

Idan za a iya tunawa Auwalu Daudawa a taba ajiye makamai tare da mika wuya ga gwamnatin Zamfara, inda ya yi alkawarin daina kai hare-hare, amma ya karya alkawarin da ya dauka ya sake daukar makamai.

Daudawa ya gamu da ajalinsa a ranar Juma’a a hannun abokan hamayyarsa a 2021.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ado AleiroKatsinaNadin SarautaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Jajantawa Ministan Harkokin Wajen Pakistan Game Da Aukuwar Ambaliyar Ruwa A Kasar

Next Post

Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

8 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

10 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.