• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masarautar ’Yandoton Daji da ke jihar Zamfara, ta nada kasurgumin dan bindigar nan da ake nema ruwa a jallo, Ado Aleiro, sarautar Sarkin Fulanin ’Yandoto a ranar Asabar.

Aleiro dan bindiga ne da ya yi kaurin suna a ciki da wajen jihar Zamfara.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna
  • Zaben Osun: ‘Yan Nijeriya Na Kallon Mu – Mahmoud Ga Ma’aikatan INEC

A baya gwamnatin Zamfara da wasu jihohi da ke makwabtaka da jihar sun yi kokarin yin sulhu da neman zaman lafiya daga hare-haren da shi da yaransa ke kai wa kauyukan jihar.

An gudanar da bikin nadin ne ’yan sa’o’i bayan masarautar ta sanar da fasa nadin tun da farko.

Sarkin na ’Yandoto, Alhaji Aliyu Marafa tun da farko ya yi shirn nada Aleiron sarautar a ranar Asabar, amma ya dage bikin ’yan sa’o’i sakamakon umarnin gwamnatin jihar, kamar yadda Aminiya ta ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Nadin na zuwa ne biyo bayan rawar da masarautar ta taka a baya tsakanin masarautar da ‘yan bindigar da suka addabi karamar hukumar tsafe a jihar.

Gwamnatin jihar dai tun da farko ta ba da umarnin dakatar da nadin ne saboda gudun cece-kucen da hakan zai iya jawowa idan labarin ya fita.

Bikin nadin sarautar dai, wanda aka yi a fadar masarautar ’Yandoton Daji, ya samu halartar Shugaban Karamar Hukumar Tsafe da kuma Kwamishinan Tsaro da Al’amuran Cikin Gida na Jihar, DIG Mamman Tsafe (mai ritaya).

Wata majiya ta shaida cewar “Bikin ya kuma samu halartar shugabannin ’yan bindiga da dama tare da dakarunsu da suka je a kan babura.

“Sun bi ta hanyar Gusau zuwa Funtuwa, inda suka yada zango a Gidan Dawa, inda mutanen garin suka ba su katan-katan na lemukan sha a matsayin gudunmawa,” inji majiyar da ta bukaci a sakaya sunanta.

“Amma babu tabbaci ko shi Aleiron ya yi jawabi yayain nadin, amma daya daga cikin na hannun damansa wanda ya yi jawabi ya koka da yadda ya ce mutane na kiransu da ’yan ta’adda,” inji mazaunin yankin da ya bayyana sunansa da Sufyan.

“Mu ba ’yan fashi ba ne kuma ba ’yan ta’adda ba, amma muddin ana so zaman lafiya ya dawo, dole gwamnatin jiha da ta tarayya su samar mana mu makiyaya da filayen kiwo da makarantu da asibitoci.,”

A baya Aleiro ya yi alkawarin ajiye makamansa, amma daga bisani ya sake kai wasu munanan hare-hare Kananan Hukumomin Tsafe da Faskari da Kankara da ke jihohin Zamfara da Katsina.

Jim kadan da yin haka ne rundunar ’yan sandan Katsina ta sanya la’adar Naira miliyan biyar ga duk wanda ya kawo mata shi.

Tun daga lokacin ne ya yi ta kitsa hare-hare a yankunan Kananan Hukumomin da ke Tsafe da kuma Faskari a jihohin biyu.

Ko a baya gwamnatin Katsina ta sha shirya zaman sulhu tsakaninta da ‘yan bindiga amma alkawarin ba ya dorewa.

Idan za a iya tunawa Auwalu Daudawa a taba ajiye makamai tare da mika wuya ga gwamnatin Zamfara, inda ya yi alkawarin daina kai hare-hare, amma ya karya alkawarin da ya dauka ya sake daukar makamai.

Daudawa ya gamu da ajalinsa a ranar Juma’a a hannun abokan hamayyarsa a 2021.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ado AleiroKatsinaNadin SarautaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Jajantawa Ministan Harkokin Wajen Pakistan Game Da Aukuwar Ambaliyar Ruwa A Kasar

Next Post

Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

5 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

11 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

16 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

20 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

21 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.