• Leadership Hausa
Saturday, March 25, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara 

by Sadiq
8 months ago
in Manyan Labarai
0
An Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masarautar ’Yandoton Daji da ke jihar Zamfara, ta nada kasurgumin dan bindigar nan da ake nema ruwa a jallo, Ado Aleiro, sarautar Sarkin Fulanin ’Yandoto a ranar Asabar.

Aleiro dan bindiga ne da ya yi kaurin suna a ciki da wajen jihar Zamfara.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna
  • Zaben Osun: ‘Yan Nijeriya Na Kallon Mu – Mahmoud Ga Ma’aikatan INEC

A baya gwamnatin Zamfara da wasu jihohi da ke makwabtaka da jihar sun yi kokarin yin sulhu da neman zaman lafiya daga hare-haren da shi da yaransa ke kai wa kauyukan jihar.

An gudanar da bikin nadin ne ’yan sa’o’i bayan masarautar ta sanar da fasa nadin tun da farko.

Sarkin na ’Yandoto, Alhaji Aliyu Marafa tun da farko ya yi shirn nada Aleiron sarautar a ranar Asabar, amma ya dage bikin ’yan sa’o’i sakamakon umarnin gwamnatin jihar, kamar yadda Aminiya ta ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

Nadin na zuwa ne biyo bayan rawar da masarautar ta taka a baya tsakanin masarautar da ‘yan bindigar da suka addabi karamar hukumar tsafe a jihar.

Gwamnatin jihar dai tun da farko ta ba da umarnin dakatar da nadin ne saboda gudun cece-kucen da hakan zai iya jawowa idan labarin ya fita.

Bikin nadin sarautar dai, wanda aka yi a fadar masarautar ’Yandoton Daji, ya samu halartar Shugaban Karamar Hukumar Tsafe da kuma Kwamishinan Tsaro da Al’amuran Cikin Gida na Jihar, DIG Mamman Tsafe (mai ritaya).

Wata majiya ta shaida cewar “Bikin ya kuma samu halartar shugabannin ’yan bindiga da dama tare da dakarunsu da suka je a kan babura.

“Sun bi ta hanyar Gusau zuwa Funtuwa, inda suka yada zango a Gidan Dawa, inda mutanen garin suka ba su katan-katan na lemukan sha a matsayin gudunmawa,” inji majiyar da ta bukaci a sakaya sunanta.

“Amma babu tabbaci ko shi Aleiron ya yi jawabi yayain nadin, amma daya daga cikin na hannun damansa wanda ya yi jawabi ya koka da yadda ya ce mutane na kiransu da ’yan ta’adda,” inji mazaunin yankin da ya bayyana sunansa da Sufyan.

“Mu ba ’yan fashi ba ne kuma ba ’yan ta’adda ba, amma muddin ana so zaman lafiya ya dawo, dole gwamnatin jiha da ta tarayya su samar mana mu makiyaya da filayen kiwo da makarantu da asibitoci.,”

A baya Aleiro ya yi alkawarin ajiye makamansa, amma daga bisani ya sake kai wasu munanan hare-hare Kananan Hukumomin Tsafe da Faskari da Kankara da ke jihohin Zamfara da Katsina.

Jim kadan da yin haka ne rundunar ’yan sandan Katsina ta sanya la’adar Naira miliyan biyar ga duk wanda ya kawo mata shi.

Tun daga lokacin ne ya yi ta kitsa hare-hare a yankunan Kananan Hukumomin da ke Tsafe da kuma Faskari a jihohin biyu.

Ko a baya gwamnatin Katsina ta sha shirya zaman sulhu tsakaninta da ‘yan bindiga amma alkawarin ba ya dorewa.

Idan za a iya tunawa Auwalu Daudawa a taba ajiye makamai tare da mika wuya ga gwamnatin Zamfara, inda ya yi alkawarin daina kai hare-hare, amma ya karya alkawarin da ya dauka ya sake daukar makamai.

Daudawa ya gamu da ajalinsa a ranar Juma’a a hannun abokan hamayyarsa a 2021.

Tags: Ado AleiroKatsinaNadin SarautaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Jajantawa Ministan Harkokin Wajen Pakistan Game Da Aukuwar Ambaliyar Ruwa A Kasar

Next Post

Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

Related

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi
Manyan Labarai

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

4 hours ago
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari
Manyan Labarai

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

6 hours ago
Yadda Na’urar BBAS Ta Sauya Salon Zaben Gwamnoni
Manyan Labarai

Yadda Na’urar BBAS Ta Sauya Salon Zaben Gwamnoni

7 hours ago
Matasan Da Za A Dama Da Su A Sabuwar Gwamnati
Manyan Labarai

Matasan Da Za A Dama Da Su A Sabuwar Gwamnati

8 hours ago
Bukatar Magance Yawaitar Hatsarin Jirgin Kasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Bukatar Magance Yawaitar Hatsarin Jirgin Kasa A Nijeriya

10 hours ago
Ban Taba Cewa Ba Zan Mika Wa Tinubu Mulki Ba -Buhari
Manyan Labarai

Ban Taba Cewa Ba Zan Mika Wa Tinubu Mulki Ba -Buhari

22 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

Da Dumi-Dumi: Tsohuwar Shugabar Mata Ta APC, Kemi Nelson, Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 4

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 4

March 25, 2023
An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

March 25, 2023
Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

March 25, 2023
Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

March 25, 2023
An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

March 25, 2023
Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

March 25, 2023
Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

March 25, 2023
Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

March 25, 2023
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

March 25, 2023
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

March 25, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.