• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar kula da ayyuka ta Nijeriya (CIPMN), ta bayyana cewa ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya a halin yanzu sun kai sama da na naira tiriliyan 17.

 

Magatakardan cibiyar CIPMN, Mista Henry Mbadiwe ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja a wani taron manema labarai.

  • Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya
  • Kwazon Kasar Sin A Ayyukan Shiga Tsakani Na Samun Yabo Daga Sassan Kasa Da Kasa

Mbadiwe ya yi nuni da cewa, binciken ya nuna cewa manyan abubuwan da ke haifar da ayyukan da aka yi watsi da su a Nijeriya sun hada da, “Rashin hangen nesa da rashin ingantaccen tsarin aikin daga farkon da rashin wadataccen kasafin kudin aikin da tsarin shari’a mara inganci da cin hanci da rashawa da hadin baki da kuma raunana cibiyoyi a Nijeriya wanda ke haifar da rashin ci gaba tare da sauye-sauye a harkokin siyasa.”

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

Ya tabbatar da cewa CIPMN za ta ci gaba da gudanar da sauye-sauyen gwamnatocin da suka shude da kuma gazawarsu tare da fara aiwatar da dokar da ta kafa cibiyar.

 

Ya ce, “Ba za mu iya ci gaba da zura ido ba muna kallon gwamnati tana barin irin wannan lamari ba.

 

“CIPMN za ta gudanar da canje-canjen gwamnatocin da suka gabata da inda suka samu rauni da kuma fara aiwatar sauye-sauye kamar yadda doka ta tanada.

 

“Za mu ci gaba da bin kadin dukkan ayyukan da aka fara aiwatarwa a Nijeriya, inda doka ta bukaci wadanda ke jagorantar wadannan ayyukan su kasance kwararrun manajojin ayyukan da CPMN ta ba su lasisi.”

 

Mbadiwe ya gargadi masu gudanar da ayyuka marasa lasisi a Nijeriya da su daina irin wannan aiki kai tsaye ko kuma su fuskanci sakamakon abin da suka aikatawa.

 

Ya ce, “Bari na bayyana muku cewa, cibiyar kula da gudanar da ayyuka ta Nijeriya ba za ta amince da manajojin ayyuka marasa lasisi suna kula da ayyuka a Nijeriya ba. Wadanda suke aikata hakan za su fuskanci mummunan hukunci.

 

“Dokar da ta kafa CIPMN ta bayyana cewa duk wanda ke cikin gwamnati da masu zaman kansu da ke shugabanta da jagorori da masu koyarwa fannin gudanar da ayyuka a Nijeriya dole ne a ba shi lasisin yin wannan sana’a.

 

“Ba shawara ba ce, doka ce, kuma muna tunanin lokaci ya yi da za mu fara bin doka a kasar nan.

 

“Daya daga cikin kalubalen da muke fuskanta a Nijeriya ba wai rashin dokoki ba ne, amma rashin mutunta wadannan dokoki ne, sau da yawa mutum zai aikata laifi kuma ya kauce wa hukunci.

 

“Duk da cewa ba mu da ikon kula da dukkan bangarorin, muna iya tabbatar muku da cewa a bangaren gudanar da ayyuka, mun himmatu wajen tabbatar da doka da oda, tare da tabbatar da cewa dukkan manajojin ayyukan suna da lasisi da kuma bin ka’idogin ayyukansu.”

 

Don haka, ya shawarci mutanen da suke da lasisin a fannin gudanar da ayyukan daga Cibiyar CIPMN da su tabbatar sun bi dokokin cibiyar yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaCin Hanci Da RashawaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Mutane Ke Tona Ramin Tururuwa Don Neman Abinci A Borno

Next Post

Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Related

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano
Manyan Labarai

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

50 minutes ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

2 hours ago
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya
Labarai

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

3 hours ago
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi
Manyan Labarai

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

5 hours ago
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil
Manyan Labarai

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

6 hours ago
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano
Manyan Labarai

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

16 hours ago
Next Post
Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

LABARAI MASU NASABA

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.