• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargabar Wasu Leburori 3 Sun Mutu Sakamakon Ƙasa Ta Rufto Musu A Nasarawa

by Muhammad
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Al'ajabi, Manyan Labarai
0
Ana Fargabar Wasu Leburori 3 Sun Mutu Sakamakon Ƙasa Ta Rufto Musu A Nasarawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana fargabar wasu leburori uku da suke aikin hakar kasa a yammacin ranar Lahadin sun mutu bayan da wata kasa ta afko kansu a wani kauye da ake kira Unguwan Ayaba da ke karamar hukumar Keffi a jihar Nasarawa.

Ma’aikatan suna ta tono jar kasa tare da loda ta a cikin wata motar dakon kasa a wurin da suke hako kasar, sai kwatsam kasar ta yanko ta afka musu ta binne mutum hudu daga cikinsu.

  • Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa
  • Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Tabbatar Da Zaɓen Sule A Matsayin Gwamnan Nasarawa

An ce daya daga cikinsu an yi sa a ya tsallake rijiya da baya domin ya samu ya tsira daga karkashin kasar da ta danne su, sai dai ya samu raunuka yayin da sauran mutum ukun har yanzu ake kan tono ba a gansu ba.

Masu aikin ceto mutanen da mazauna kauyukan da suka hada da ‘yan uwan ​​wadanda abin ya shafa sun killace wurin domin tono gawarwakin ma’aikatan uku, sun fara aikin tonon tun da yammacin ranar Lahadi lokacin da abun ya faru, amma abin ya ci tura har zuwa lokacin kawo wannan rahoton.

Daya daga cikin masu aikin sa kai a wurin, Saliu Abdullahi, ya ce sun shafe fiye da sa’o’i biyu suna aikin tono ma’aikatan, ya kara da cewa ba za su bar wurin ba har sai sun hako gawarwakin ma’aikatan uku.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Shima mataimakin shugaban kungiyar masu Tipper da ke karamar hukumar Keffi, Aminu Sunusi, ya ce sun aika da injin tona domin a samu a gaggauta aikin ceto mutanen.

Sunusi ya kara da cewa za su dauki kwararan matakai don kaucewa irin matsalar da ake ciki da dakile afkuwar irin wannan hadari a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KasaNasarawaRuftawaRuftowar kasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi: Sin Na Fatan Hade Dabarun Raya Kasa Da Jamaica

Next Post

AFCON 2023: Afirika Ta Kudu Ta Lallasa Ƙasar Namibiya Da Ci 4-0

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

19 minutes ago
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

2 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

5 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

10 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

14 hours ago
Next Post
AFCON 2023: Afirika Ta Kudu Ta Lallasa Ƙasar Namibiya Da Ci 4-0

AFCON 2023: Afirika Ta Kudu Ta Lallasa Ƙasar Namibiya Da Ci 4-0

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.